< Proverbes 7 >
1 Mon fils, garde mes paroles, et mets en réserve par-devers toi mes commandements.
Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
2 Garde mes commandements, et tu vivras, et garde mon enseignement comme la prunelle de tes yeux.
Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
3 Lie-les à tes doigts, écris-les sur la table de ton cœur.
Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Dis à la sagesse: Tu es ma sœur; et appelle la prudence, ta parente.
Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
5 Afin qu'elles te gardent de la femme étrangère, et de la foraine, qui se sert de paroles flatteuses.
za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
6 Comme je regardais à la fenêtre de ma maison par mes treillis,
A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
7 Je vis entre les sots, et je considérai entre les jeunes gens un jeune homme dépourvu de sens,
Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
8 Qui passait par une rue, près du coin d'une certaine femme, et qui tenait le chemin de sa maison;
Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
9 Sur le soir à la fin du jour, lorsque la nuit devenait noire et obscure.
da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
10 Et voici, une femme vint au-devant de lui, parée en femme de mauvaise vie, et pleine de ruse;
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
11 Bruyante et débauchée, et dont les pieds ne demeurent point dans sa maison;
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
12 Etant tantôt dehors, et tantôt dans les rues, et se tenant aux aguets à chaque coin de rue.
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
13 Elle le prit, et le baisa; et avec un visage effronté, lui dit:
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
14 J'ai chez moi des sacrifices de prospérité; j'ai aujourd'hui payé mes vœux.
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
15 C'est pourquoi je suis sortie au-devant de toi, pour te chercher soigneusement, et je t'ai trouvé.
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
16 J'ai garni mon lit d'un tour de réseau, entrecoupé de fil d'Egypte.
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
17 Je l'ai parfumé de myrrhe, d'aloès et de cinnamome.
Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
18 Viens, enivrons-nous de plaisir jusqu'au matin, réjouissons-nous en amours.
Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
19 Car mon mari n'est point en sa maison; il s'en est allé en voyage bien loin.
Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
20 Il a pris avec soi un sac d'argent; il retournera en sa maison au jour assigné.
Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
21 Elle l'a fait détourner par beaucoup de douces paroles, et l'a attiré par la flatterie de ses lèvres.
Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
22 Il s'en est aussitôt allé après elle, comme le bœuf s'en va à la boucherie, et comme le fou, aux ceps pour être châtié;
Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
23 Jusqu'à ce que la flèche lui ait transpercé le foie; comme l'oiseau qui se hâte vers le filet, ne sachant point qu'on l'a tendu contre sa vie.
sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
24 Maintenant donc, enfants, écoutez-moi, et soyez attentifs à mes discours.
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
25 Que ton cœur ne se détourne point vers les voies de cette femme, et qu'elle ne te fasse point égarer dans ses sentiers.
Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
26 Car elle a fait tomber plusieurs blessés à mort, et tous ceux qu'elle a tués étaient forts.
Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
27 Sa maison sont les voies du sépulcre, qui descendent aux cabinets de la mort. (Sheol )
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol )