< Proverbes 6 >

1 Mon fils, si tu as cautionné [pour quelqu'un] envers ton ami, ou si tu as frappé dans la main à l'étranger,
Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
2 Tu es enlacé par les paroles de ta bouche, tu es pris par les paroles de ta bouche.
in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
3 Mon fils, fais maintenant ceci, et te dégage, puisque tu es tombé entre les mains de ton intime ami, va, prosterne-toi, et encourage tes amis.
to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
4 Ne donne point de sommeil à tes yeux, et ne laisse point sommeiller tes paupières.
Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
5 Dégage-toi comme le daim de la main [du chasseur], et comme l'oiseau de la main de l'oiseleur.
Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
6 Va, paresseux, vers la fourmi, regarde ses voies, et sois sage.
Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
7 Elle n'a ni chef, ni directeur, ni gouverneur,
Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
8 [Et cependant] elle prépare en été son pain, et amasse durant la moisson de quoi manger.
duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
9 Paresseux, jusqu'à quand te tiendras-tu couché? Quand te lèveras-tu de ton lit?
Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
10 Un peu de sommeil, [dis-tu], un peu de sommeil, un peu de ploiement de bras, afin de demeurer couché;
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
11 Et ta pauvreté viendra comme un passant; et ta disette, comme un soldat.
talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
12 L'homme qui imite le démon, est un homme violent et ses discours sont faux.
Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
13 Il fait signe de ses yeux, il parle de ses pieds, il enseigne de ses doigts.
wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
14 Il y a des renversements dans son cœur, il machine du mal en tout temps, il fait naître des querelles.
wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
15 C'est pourquoi sa calamité viendra subitement, il sera subitement brisé, il n'y aura point de guérison.
Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
16 Dieu hait ces six choses, et même sept lui sont en abomination;
Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
17 Savoir, les yeux hautains, la fausse langue, les mains qui répandent le sang innocent;
duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
18 Le cœur qui machine de mauvais desseins; les pieds qui se hâtent pour courir au mal;
zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
19 Le faux témoin qui profère des mensonges; et celui qui sème des querelles entre les frères.
mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
20 Mon fils, garde le commandement de ton père, et n'abandonne point l'enseignement de ta mère;
Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
21 Tiens-les continuellement liés à ton cœur, et les attache à ton cou.
Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
22 Quand tu marcheras, il te conduira; et quand tu te coucheras, il te gardera; et quand tu te réveilleras, il s'entretiendra avec toi.
Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
23 Car le commandement est une lampe; et l'enseignement une lumière; et les répréhensions propres à instruire [sont] le chemin de la vie.
Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
24 Pour te garder de la mauvaise femme, et des flatteries de la langue étrangère,
suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
25 Ne convoite point en ton cœur sa beauté, et ne te laisse point prendre à ses yeux.
Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
26 Car pour l'amour de la femme débauchée on en vient jusqu'à un morceau de pain, et la femme [convoiteuse] d'homme chasse après l'âme précieuse [de l'homme.]
Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
27 Quelqu'un peut-il prendre du feu dans son sein, sans que ses habits brûlent?
Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
28 Quelqu'un marchera-t-il sur la braise, sans que ses pieds en soient brûlés?
Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
29 Ainsi [en prend-il] à celui qui entre vers la femme de son prochain; quiconque la touchera, ne sera point innocent.
Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
30 On ne méprise point un larron, s'il dérobe pour remplir son âme, quand il a faim;
Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
31 Et s'il est trouvé, il le récompensera sept fois au double, il donnera tout ce qu'il a dans sa maison.
Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
32 [Mais] celui qui commet adultère avec une femme, est dépourvu de sens; et celui qui le fera, sera le destructeur de son âme.
Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
33 Il trouvera des plaies et de l'ignominie, et son opprobre ne sera point effacé.
Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
34 Car la jalousie est une fureur de mari, qui n'épargnera point [l'adultère] au jour de la vengeance.
Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
35 Il n'aura égard à aucune rançon, et il n'acceptera rien, quand tu multiplierais les présents.
Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.

< Proverbes 6 >