< Proverbes 2 >

1 Mon fils, si tu reçois mes paroles, et que tu mettes en réserve par-devers toi mes commandements;
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 Tellement que tu rendes ton oreille attentive à la sagesse, et que tu inclines ton cœur à l'intelligence;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 Si tu appelles à toi la prudence, et que tu adresses ta voix à l'intelligence;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 Si tu la cherches comme de l'argent, et si tu la recherches soigneusement comme des trésors;
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Alors tu connaîtras la crainte de l'Eternel, et tu trouveras la connaissance de Dieu.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Car l'Eternel donne la sagesse; et de sa bouche procède la connaissance et l'intelligence.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 Il réserve pour ceux qui sont droits un état permanent, et il est le bouclier de ceux qui marchent dans l'intégrité;
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 Pour garder les sentiers de jugement; [tellement qu'] il gardera la voie de ses bien-aimés.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Alors tu entendras la justice, et le jugement, et l'équité, et tout bon chemin.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Si la sagesse vient en ton cœur, et si la connaissance est agréable à ton âme;
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 La prudence te conservera, et l'intelligence te gardera;
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 Pour te délivrer du mauvais chemin, et de l'homme prononçant de mauvais discours.
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 De ceux qui laissent les chemins de la droiture pour marcher par les voies de ténèbres;
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Qui se réjouissent à mal faire, et s'égayent dans les renversements que fait le méchant.
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Desquels les chemins sont tortus, et qui vont de travers en leur train.
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 [Et] afin qu'il te délivre de la femme étrangère, et de la femme d'autrui, dont les paroles sont flatteuses;
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 Qui abandonne le conducteur de sa jeunesse, et qui a oublié l'alliance de son Dieu.
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 Car sa maison penche vers la mort, et son chemin mène vers les trépassés.
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Pas un de ceux qui vont vers elle, n'en retourne, ni ne reprend les sentiers de la vie.
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Afin aussi que tu marches dans la voie des gens de bien, et que tu gardes les sentiers des justes.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Car ceux qui sont justes habiteront en la terre, et les hommes intègres demeureront de reste en elle.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 Mais les méchants seront retranchés de la terre, et ceux qui agissent perfidement en seront arrachés.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Proverbes 2 >