< Nombres 1 >
1 Or l'Eternel parla à Moïse au désert de Sinaï, dans le Tabernacle d'assignation, le premier jour du second mois de la seconde année, après qu'ils furent sortis du pays d'Egypte, en disant:
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Faites le dénombrement de toute l'assemblée des enfants d'Israël, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, en les comptant nom par nom, [savoir] tous les mâles, chacun par tête;
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 Depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux d'Israël qui peuvent aller à la guerre, vous les compterez suivant leurs troupes, toi et Aaron.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 Et il y aura avec vous un homme de chaque Tribu, [savoir] celui qui [est] le chef de la maison de ses pères.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 Et ce sont ici les noms de ces hommes qui vous assisteront. Pour la Tribu de Ruben, Elitsur fils de Sédéur.
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 Pour celle de Siméon, Sélumiel, fils de Tsurisaddaï.
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 Pour celle de Juda, Nahasson, fils de Hamminadab.
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Pour celle d'Issacar, Nathanaël, fils de Tsuhar.
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 Pour celle de Zabulon, Eliab, fils de Hélon.
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 des enfants de Joseph, pour la Tribu d'Ephraïm, Elisamah, fils de Hammiud; pour celle de Manassé, Gamaliel fils de Pédatsur.
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 Pour la Tribu de Benjamin, Abidan, fils de Guidhoni.
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 Pour celle de Dan, Ahihézer, fils de Hammisaddaï.
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 Pour celle d'Aser, Paghiel, fils de Hocran.
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 Pour celle de Gad, Eliasaph, fils de Déhuël.
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Pour celle de Nephthali, Ahirah, fils de Hénan.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 C'étaient là ceux qu'on appelait pour tenir l'assemblée; ils étaient les principaux des Tribus de leurs pères, chefs des milliers d'Israël.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 Alors Moïse et Aaron prirent ces hommes-là qui avaient été nommés par leurs noms;
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 Et ils convoquèrent toute l'assemblée, le premier jour du second mois, et on enregistra chacun selon leurs familles, [et] selon la maison de leurs pères, les enregistrant, nom par nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, chacun par tête;
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 Comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse, il les dénombra au désert de Sinaï.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 Les enfants donc de Ruben, premier-né d'Israël, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dont on fit le dénombrement par leur nom, [et] par tête, [savoir] tous les mâles de l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Ruben, qui furent dénombrés, furent quarante-six mille cinq cents.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Des enfants de Siméon, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, ceux qui furent dénombrés par leur nom et par tête, [savoir] tous les mâles de l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Siméon, qui furent dénombrés, furent cinquante-neuf mille trois cents.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Des enfants de Gad, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 Ceux, [ dis-je], de la Tribu de Gad, qui furent dénombrés, furent quarante-cinq mille six cent cinquante.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Des enfants de Juda, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Juda, qui furent dénombrés, furent soixante et quatorze mille six cents.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Des enfants d'Issacar, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 Ceux, [dis-je], de la Tribu d'Issacar, qui furent dénombrés, furent cinquante-quatre mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Des enfants de Zabulon, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Zabulon, qui furent dénombrés, furent cinquante-sept mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Quant aux enfants de Joseph; les enfants d'Ephraïm, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 Ceux, [dis-je], de la Tribu d'Ephraïm, qui furent dénombrés, furent quarante mille cinq cents.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Des enfants de Manassé, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Manassé, qui furent dénombrés, furent trente-deux mille deux cents.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Des enfants de Benjamin, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Benjamin, qui furent dénombrés, furent trente-cinq mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Des enfants de Dan, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Dan, qui furent dénombrés, furent soixante-deux mille sept cents.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Des enfants d'Aser, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 Ceux, [dis-je], de la Tribu d'Aser, qui furent dénombrés, furent quarante et un mille cinq cents.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 [Des] enfants de Nephthali, selon leurs générations, leurs familles, et les maisons de leurs pères, dénombrés chacun par leur nom, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux qui pouvaient aller à la guerre;
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 Ceux, [dis-je], de la Tribu de Nephthali, qui furent dénombrés, furent cinquante-trois mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 Ce sont là ceux dont Moïse et Aaron firent le dénombrement, les douze principaux [d'entre les enfants] d'Israël y étant, un pour chaque maison de leurs pères.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 Ainsi tous ceux des enfants d'Israël, dont on fit le dénombrement, selon les maisons de leurs pères, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, tous ceux d'entre les Israélites, qui pouvaient aller à la guerre;
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 Tous ceux, [dis-je], dont on fit le dénombrement, furent six cent trois mille cinq cent cinquante.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 Mais les Lévites ne furent point dénombrés avec eux, selon la Tribu de leurs pères.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 Car l'Eternel avait parlé à Moïse, en disant:
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 Tu ne feras aucun dénombrement de la Tribu de Lévi, et tu n'en lèveras point la somme avec les [autres] enfants d'Israël.
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 Mais tu donneras aux Lévites la charge du pavillon du Témoignage, et de tous ses ustensiles, et de tout ce qui lui appartient; ils porteront le pavillon, et tous ses ustensiles; ils y serviront, et camperont autour du pavillon.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 Et quand le pavillon partira, les Lévites le désassembleront, et quand le pavillon campera, ils le dresseront. Que si quelque étranger en approche, on le fera mourir.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 Or les enfants d'Israël camperont chacun en son quartier, et chacun sous son enseigne, selon leurs troupes.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 Mais les Lévites camperont autour du pavillon du Témoignage, afin qu'il n'y ait point d'indignation sur l'assemblée des enfants d'Israël, et ils prendront en leur charge le pavillon du Témoignage.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 Et les enfants d'Israël firent selon toutes les choses que l'Eternel avait commandées à Moïse; ils le firent ainsi.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.