< Nombres 8 >

1 L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Parle à Aaron, et lui dis: Quand tu allumeras les lampes, les sept lampes éclaireront sur le devant du chandelier.
“Yi magana da Haruna, ka ce masa, ‘Sa’ad da za ka shisshirya fitilun nan bakwai, ka shirya su yadda za su fuskanci gaba domin haskensu yă haskaka ta gaba.’”
3 Et Aaron le fit ainsi, et il alluma les lampes [pour éclairer] sur le devant du chandelier, comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse.
Haka kuwa Haruna ya yi; ya shisshirya fitilun yadda za su fuskanci gaba a kan wurin ajiye fitilan, kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
4 Or le chandelier était fait de telle manière, qu'il était d'or battu au marteau, [d'ouvrage] fait au marteau, sa tige aussi, [et] ses fleurs. On fit ainsi le chandelier selon le modèle que l'Eternel en avait fait voir à Moïse.
Ga yadda aka yi wurin ajiye fitilan. An ƙera shi da zinariya daga gindinsa har zuwa sama inda ya buɗu. Aka ƙera wurin ajiye fitilan yadda Ubangiji ya nuna wa Musa.
5 Puis l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
6 Prends les Lévites d'entre les enfants d'Israël, et les purifie.
“Keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, ka tsarkake su.
7 Tu leur feras ainsi pour les purifier. Tu feras aspersion sur eux de l'eau de purification; ils feront passer le rasoir sur toute leur chair, ils laveront leurs vêtements, et ils se purifieront.
Ga yadda za ka tsarkake su, ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa; ka sa su aske jikunansu duka su kuma wanke tufafinsu, ta haka za su tsarkake kansu.
8 Puis ils prendront un veau pris du troupeau avec son gâteau de fine farine pétrie à l'huile; et tu prendras un second veau pris du troupeau [pour l'offrande] pour le péché.
Ka sa su ɗauki ɗan bijimi tare da lallausan garin hadaya, kwaɓaɓɓe da mai; sa’an nan, kai kuma ka ɗauki ɗan bijimi na biyu na hadaya don zunubi.
9 Alors tu feras approcher les Lévites devant le Tabernacle d assignation, et tu convoqueras toute l'assemblée des enfants d'Israël.
Ka kawo Lawiyawa a gaban Tentin Sujada, ka kuma kira taron Isra’ilawa duka.
10 Tu feras, [dis-je], approcher les Lévites devant l'Eternel, et les enfants d'Israël poseront leurs mains sur les Lévites.
Za ka kawo Lawiyawa a gaban Ubangiji, Isra’ilawa kuma za su ɗibiya musu hannuwansu.
11 Et Aaron présentera les Lévites en offrande devant l'Eternel de la part des enfants d'Israël, et ils seront employés au service de l'Eternel.
Haruna zai miƙa Lawiyawa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa daga Isra’ilawa, saboda a shirya su domin aikin Ubangiji.
12 Et les Lévites poseront leurs mains sur la tête des veaux; puis tu en sacrifieras l'un [en offrande] pour le péché, et l'autre en holocauste à l'Eternel, afin de faire propitiation pour les Lévites.
“Bayan Lawiyawa sun ɗibiya hannuwansu a kan bijiman, sai ka yi amfani da ɗaya a matsayin hadaya don zunubi ga Ubangiji, ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa, don yin kafara saboda Lawiyawa.
13 Après tu feras tenir les Lévites devant Aaron et devant ses fils, et tu les présenteras en offrande à l'Eternel.
Ka kuma sa Lawiyawa su tsaya a gaban Haruna da’ya’yansa, sai ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji.
14 Ainsi tu sépareras les Lévites d'entre les enfants d'Israël, et les Lévites seront à moi.
Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, Lawiyawa za su zama nawa.
15 Après cela les Lévites viendront pour servir au Tabernacle d'assignation, quand tu les auras purifiés, et présentés en offrande.
“Bayan ka tsarkake Lawiyawa, ka kuma miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, sai su zo su yi aikinsu a Tentin Sujada.
16 Car ils me sont entièrement donnés d'entre les enfants d'Israël; je les ai pris pour moi au lieu de tous ceux qui ouvrent la matrice, au lieu de tous les premiers-nés d'entre les enfants d'Israël.
Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra’ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato, dukan’ya’yan farin Isra’ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa.
17 Car tout premier-né d'entre les enfants d'Israël est à moi, tant des hommes que des bêtes; je me les suis sanctifiés le jour que je frappai tout premier-né au pays d'Egypte.
Kowane ɗan farin haihuwa, ko mutum, ko dabba a Isra’ila, nawa ne. Sa’ad da na kashe’ya’yan fari a Masar, na keɓe’ya’yan fari na Isra’ilawa wa kaina.
18 r j'ai pris les Lévites au lieu de tous les premiers-nés d'entre les enfants d'Israël.
Na kuma ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari maza a Isra’ila.
19 Et j'ai entièrement donné d'entre les enfants d'Israël les Lévites à Aaron et à ses fils, pour faire le service des enfants d'Israël dans le Tabernacle d'assignation, et pour servir de rachat pour les enfants d'Israël; afin qu'il n'y ait point de plaie sur les enfants d'Israël, [comme il y aurait] si les enfants d'Israël s'approchaient du Sanctuaire.
Cikin dukan Isra’ilawa, na ba da Lawiyawa kyauta ga Haruna da’ya’yansa, su yi hidima a Tentin Sujada a madadin Isra’ilawa, su kuma yi kafara dominsu saboda kada annoba ta bugi Isra’ilawa sa’ad da suka je kusa da wuri mai tsarki.”
20 Moïse et Aaron, et toute l'assemblée des enfants d'Israël firent aux Lévites toutes les choses que l'Eternel avait commandées à Moïse touchant les Lévites; les enfants d'Israël le firent ainsi.
Musa, Haruna da kuma dukan taron Isra’ilawa, suka yi da Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
21 Les Lévites donc se purifièrent, et lavèrent leurs vêtements, et Aaron les présenta en offrande devant l'Eternel, et fit propitiation pour eux afin de les purifier.
Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma wanke tufafinsu. Sai Haruna ya miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa a gaban Ubangiji, ya kuma yi kafara saboda su don yă tsarkake su.
22 Cela étant fait, les Lévites vinrent pour faire leur service au Tabernacle d'assignation devant Aaron, et devant ses fils; et on leur fit comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse touchant les Lévites.
Bayan haka, sai Lawiyawa suka zo don su yi aikinsu a Tentin Sujada, a ƙarƙashin Haruna da’ya’yansa. Suka yi da Lawiyawa kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
23 Puis l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
24 C'est ici ce qui concerne les Lévites. Le Lévite depuis l'âge de vingt-cinq ans et au dessus, entrera en service pour être employé au Tabernacle d'assignation;
“Wannan ya shafi Lawiyawa ne, wato, mazan da suka kai shekara ashirin da biyar, ko fiye, za su zo su yi aiki a Tentin Sujada,
25 Mais depuis l'âge de cinquante ans il sortira de service, et ne servira plus.
amma in suka kai shekaru hamsin da haihuwa, dole su huta daga wannan aiki na yau da kullum, su kuma daina aiki.
26 Cependant il servira ses frères au Tabernacle d'assignation, pour garder ce qui [leur a été commis], mais il ne fera aucun service; tu feras donc ainsi aux Lévites touchant leurs charges.
Za su iya taimakon’yan’uwansu cikin tafiyar da ayyuka a Tentin Sujada, amma su kansu ba za su yi aikin ba. Haka fa za ka ba wa Lawiyawa aikinsu.”

< Nombres 8 >