< Nombres 32 >

1 Or les enfants de Ruben et les enfants de Gad avaient beaucoup de bétail, et en fort grande quantité; et ayant vu le pays de Jahzer, et le pays de Galaad, voici, [ils remarquèrent que] ce lieu-là était propre à tenir du bétail.
Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
2 Ainsi les enfants de Gad et les enfants de Ruben vinrent, et parlèrent à Moïse et à Eléazar le Sacrificateur, et aux principaux de l'assemblée, en disant:
Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
3 Hataroth, et Dibon, et Jahzer, et Nimrah, et Hesbon, et Elhaleh, et Sébam, et Nébo, et Béhon;
“Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
4 Ce pays-là, que l'Eternel a frappé devant l'assemblée d'Israël, est un pays propre à tenir du bétail, et tes serviteurs ont du bétail.
ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
5 Ils dirent donc: Si nous avons trouvé grâce devant toi, que ce pays soit donné à tes serviteurs en possession; [et] ne nous fais point passer le Jourdain.
Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
6 Mais Moïse répondit aux enfants de Gad, et aux enfants de Ruben: Vos frères iront-ils à la guerre, et vous demeurerez-vous ici?
Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
7 Pourquoi faites-vous perdre courage aux enfants d'Israël, pour ne point passer au pays que l'Eternel leur a donné?
Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
8 C'est ainsi que firent vos pères quand je les envoyai de Kadès-barné pour reconnaître le pays.
Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
9 Car ils montèrent jusqu'à la vallée d'Escol, et virent le pays, puis ils firent perdre courage aux enfants d'Israël, afin qu'ils n'entrassent point au pays que l'Eternel leur avait donné.
Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
10 C'est pourquoi la colère de l'Eternel s'enflamma en ce jour-là, et il jura, en disant:
A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
11 Si les hommes qui sont montés [hors] d'Egypte, depuis l'âge de vingt ans, et au dessus, voient le pays pour lequel j'ai juré à Abraham, à Isaac, et à Jacob; car ils n'ont point persévéré à me suivre.
‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
12 Excepté Caleb, fils de Jéphunné Kénisien, et Josué fils de Nun; car ils ont persévéré à suivre l'Eternel.
ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
13 Ainsi la colère de l'Eternel s'enflamma contre Israël, et il les a fait errer par le désert, quarante ans, jusqu'à ce que toute la génération qui avait fait ce qui déplaisait à l'Eternel, ait été consumée.
Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
14 Et voici, vous vous êtes mis en la place de vos pères, comme une race d'hommes pécheurs, pour augmenter encore l'ardeur de la colère de l'Eternel contre Israël.
“Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
15 Que si vous vous détournez de lui, il continuera encore à le laisser au désert, et vous ferez détruire tout ce peuple.
In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
16 Mais ils s'approchèrent de lui, et lui dirent: Nous bâtirons ici des cloisons pour nos troupeaux, et les villes seront pour nos familles.
Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
17 Et nous nous équiperons pour marcher promptement devant les enfants d'Israël, jusqu'à ce que nous les ayons introduits en leur lieu; mais nos familles demeureront dans les villes murées, à cause des habitants du pays.
Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
18 Nous ne retournerons point en nos maisons que chacun des enfants d'Israël n'ait pris possession de son héritage;
Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
19 Et nous ne posséderons rien en héritage avec eux au delà du Jourdain, ni plus avant; parce que notre héritage nous sera échu au deçà du Jourdain vers l'Orient.
Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
20 Et Moïse leur dit: Si vous faites cela, et que vous vous équipiez devant l'Eternel pour aller à la guerre;
Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
21 Et que chacun de vous étant équipé passe le Jourdain devant l'Eternel, jusqu'à ce qu'il ait chassé ses ennemis de devant soi;
in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
22 Et que le pays soit subjugué devant l'Eternel, et qu'ensuite vous vous en retourniez, alors vous serez innocents envers l'Eternel, et envers Israël; et ce pays-ci vous appartiendra pour le posséder devant l'Eternel.
to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
23 Mais si vous ne faites point cela, voici, vous aurez péché contre l'Eternel; et sachez que votre péché vous trouvera.
“Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
24 Bâtissez donc des villes pour vos familles; et des cloisons pour vos troupeaux, et faites ce que vous avez dit.
Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
25 Alors les enfants de Gad, et les enfants de Ruben parlèrent à Moïse, en disant: Tes serviteurs feront comme mon Seigneur l'a commandé.
Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
26 Nos petits enfants, nos femmes, nos troupeaux, et toutes nos bêtes demeureront ici dans les villes de Galaad.
’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
27 Et tes serviteurs passeront chacun armé pour aller à la guerre devant l'Eternel, prêts à combattre, comme mon Seigneur a parlé.
Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
28 Alors Moïse commanda touchant eux à Eléazar le Sacrificateur, à Josué, fils de Nun, et aux chefs des pères des Tribus des enfants d'Israël;
Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
29 Et leur dit: Si les enfants de Gad et les enfants de Ruben passent avec vous le Jourdain tous armés, prêts à combattre devant l'Eternel, et que le pays vous soit assujetti, vous leur donnerez le pays de Galaad en possession.
ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
30 Mais s'ils ne passent point en armes avec vous, ils auront une possession parmi vous au pays de Canaan.
Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
31 Et les enfants de Gad, et les enfants de Ruben répondirent, en disant: Nous ferons ainsi que l'Eternel a parlé à tes serviteurs.
Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
32 Nous passerons en armes devant l'Eternel au pays de Canaan, afin que nous possédions pour notre héritage ce qui est deçà le Jourdain.
Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
33 Ainsi Moïse donna aux enfants de Gad, et aux enfants de Ruben, et à la demi-Tribu de Manassé, fils de Joseph, le Royaume de Sihon, Roi des Amorrhéens; et le Royaume de Hog, Roi de Basan, le pays avec ses villes, selon les bornes des villes du pays à l'environ.
Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
34 Alors les enfants de Gad rebâtirent Dibon, Hataroth, Haroher,
Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
35 Hatroth-Sophan, Jahzer, Jogbéha,
Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
36 Beth-nimrah, et Beth-haran, villes murées. Ils firent aussi des cloisons pour les troupeaux.
Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
37 Et les enfants de Ruben rebâtirent Hesbon, Elhalé, Kirjathajim,
Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
38 Nébo, et Bahal-méhon, et Sibma; dont ils changèrent les noms, et ils donnèrent des noms aux villes qu'ils rebâtirent.
haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
39 Or les enfants de Makir, fils de Manassé, allèrent en Galaad, et le prirent, et dépossédèrent les Amorrhéens qui y étaient.
Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
40 Moïse donc donna Galaad à Makir, fils de Manassé, qui y habita.
Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
41 Jaïr aussi fils de Manassé, s'en alla, et prit leurs bourgs, et les appela bourgs de Jaïr.
Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
42 Et Nobah s'en alla, et prit Kénath avec les villes de son ressort, et l'appela Nobah de son nom.
Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.

< Nombres 32 >