< Nombres 16 >
1 Or Coré, fils de Jitshar, fils de Kéhath, fils de Lévi, fit une entreprise, avec Dathan et Abiram enfants d'Eliab, et On, fils de Péleth, enfants de Ruben;
Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
2 Et ils s'élevèrent contre Moïse, avec deux cent cinquante hommes des enfants d'Israël, qui étaient des principaux de l'assemblée, lesquels on appelait pour tenir le conseil, et qui étaient des gens de réputation.
suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
3 Et ils s'assemblèrent contre Moïse et contre Aaron, et leur dirent: Qu'il vous suffise, puisque tous ceux de l'assemblée sont saints, et que l'Eternel est au milieu d'eux, pourquoi vous élevez-vous par dessus l'assemblée de l'Eternel?
tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
4 Ce que Moïse ayant entendu, il se prosterna le visage [contre terre].
Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
5 Et il parla à Coré et à tous ceux qui étaient assemblés avec lui, [et] leur dit: [Demain] au matin l'Eternel donnera à connaître celui qui lui appartient, et celui qui est le saint, et il le fera approcher de lui; il fera, dis-je, approcher de lui celui qu'il aura choisi.
Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
6 Faites ceci, prenez-vous des encensoirs; que Coré, [dis-je], et tous ceux qui sont assemblés avec lui, [prennent des encensoirs].
Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
7 Et demain mettez-y du feu, et mettez-y du parfum devant l'Eternel; et l'homme que l'Eternel aura choisi sera le saint. Enfants de Lévi; qu'il vous suffise.
ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
8 Moïse dit aussi à Coré: Ecoutez maintenant, enfants de Lévi.
Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
9 Est-ce trop peu de chose pour vous que le Dieu d'Israël vous ait séparés de l'assemblée d'Israël, en vous faisant approcher de lui pour être employés au service du pavillon de l'Eternel, et pour assister devant l'assemblée afin de la servir?
Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
10 Et qu'il t'ait fait approcher, [toi] et tous tes frères, les enfants de Lévi, avec toi, que vous recherchiez encore la Sacrificature?
Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
11 C'est pourquoi toi, et tous ceux qui sont assemblés avec toi, vous vous [êtes] assemblés contre l'Eternel; car qui est Aaron que vous murmuriez contre lui?
Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
12 Et Moïse envoya appeler Dathan et Abiram, enfants d'Eliab, qui répondirent: Nous n'y monterons point.
Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
13 Est-ce peu de chose que tu nous aies fait monter hors d'un pays découlant de lait et de miel, pour nous faire mourir dans ce désert, que même tu veuilles dominer sur nous?
Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
14 Nous as-tu fait venir en un pays découlant de lait et de miel; et nous as-tu donné quelque héritage de champs ou de vignes? crèveras-tu les yeux de ces gens-ici? nous n'y monterons point.
Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
15 Alors Moïse fut fort irrité, et dit à l'Eternel: Ne regarde point à leur offrande; je n'ai point pris d'eux un seul âne, et je n'ai point fait de mal à aucun d'eux.
Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
16 Puis Moïse dit à Coré: Toi et tous ceux qui sont assemblés avec toi, trouvez-vous demain devant l'Eternel, toi, [dis-je], et ceux-ci; et Aaron aussi.
Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
17 Et prenez chacun vos encensoirs, et mettez-y du parfum; et que chacun présente devant l'Eternel son encensoir, qui seront deux cent cinquante encensoirs; et toi et Aaron aussi, chacun avec son encensoir.
Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
18 Ils prirent donc chacun son encensoir, et y mirent du feu, et ensuite du parfum, et ils se tinrent à l'entrée du Tabernacle d'assignation, et Moïse et Aaron s'y tinrent aussi.
Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
19 Et Coré fit assembler contr'eux toute l'assemblée à l'entrée du Tabernacle d'assignation; et la gloire de l'Eternel apparut à toute l'assemblée.
Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
20 Puis l'Eternel parla à Moïse et à Aaron, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
21 Séparez-vous du milieu de cette assemblée, et je les consumerai en un moment.
“Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
22 Mais ils se prosternèrent le visage [contre terre], et dirent: Ô [Dieu] Fort? Dieu des esprits de toute chair? un seul homme aura péché, et te mettras-tu en colère contre toute l'assemblée?
Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
23 Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
24 Parle à l'assemblée, et lui dis: retirez-vous d'auprès des pavillons de Coré, de Dathan, et d'Abiram.
“Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
25 Moïse donc se leva et s'en alla vers Dathan et Abiram; et les Anciens d'Israël le suivirent.
Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
26 Et il parla à l'assemblée, en disant: Retirez-vous, je vous prie, d'auprès des tentes de ces méchants hommes, et ne touchez à rien qui leur appartienne, de peur que vous ne soyez consumés pour tous leurs péchés.
Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
27 Ils se retirèrent donc d'auprès des pavillons de Coré, de Dathan et d'Abiram. Et Dathan et Abiram sortirent; et se tinrent debout à l'entrée de leurs tentes, avec leurs femmes, leurs enfants, et leurs familles.
Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
28 Et Moïse dit: Vous connaîtrez à ceci que l'Eternel m'a envoyé pour faire toutes ces choses-là, et que je n'ai rien fait de moi-même.
Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
29 Si ceux-là meurent comme tous les hommes meurent, et s'ils sont punis de la punition de tous les hommes, l'Eternel ne m'a point envoyé.
In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
30 Mais si l'Eternel crée un cas tout nouveau, et que la terre ouvre sa bouche, et les engloutisse avec tout ce qui leur appartient, et qu'ils descendent tout vifs dans le gouffre; alors vous saurez que ces hommes-là ont irrité par mépris l'Eternel. (Sheol )
Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol )
31 Et il arriva qu'aussitôt qu'il eut achevé de dire toutes ces paroles, la terre qui était sous eux, se fendit.
Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
32 Et la terre ouvrit sa bouche, et les engloutit, avec leurs tentes, et tous les hommes qui étaient à Coré, et tout leur bien.
ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
33 Ils descendirent donc tout vifs dans le gouffre, eux, et tous ceux qui étaient à eux; et la terre les couvrit, et ils périrent au milieu de l'assemblée. (Sheol )
Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol )
34 Et tout Israël qui était autour d'eux, s'enfuit à leur cri; car ils disaient: [Prenons garde] que la terre ne nous engloutisse.
Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
35 Et le feu sortit de part de l'Eternel, et consuma les deux cent cinquante hommes qui offraient le parfum.
Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
36 Puis l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
37 Dis à Eléazar fils d'Aaron, Sacrificateur, qu'il relève les encensoirs du milieu de l'incendie, et qu'on en épande le feu au loin, car ils sont sanctifiés;
“Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
38 [Savoir] les encensoirs de ceux qui ont péché sur leurs âmes, et qu'on en fasse des plaques larges pour couvrir l'autel; puisqu'ils les ont offerts devant l'Eternel ils seront sanctifiés, et ils seront pour signe aux enfants d'Israël.
gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
39 Ainsi Eléazar Sacrificateur prit les encensoirs d'airain, que ces hommes qui furent brûlés avaient présentés, et on en fit des plaques pour couvrir l'autel.
Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
40 C'est un mémorial pour les enfants d'Israël, afin qu'aucun étranger qui n'est pas de la race d'Aaron, ne s'approche point pour faire le parfum en la présence de l'Eternel, et qu'il ne soit comme Coré, et comme ceux qui ont été assemblés avec lui; ainsi que l'Eternel en a parlé par le moyen de Moïse.
yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
41 Or dès le lendemain toute l'assemblée des enfants d'Israël murmura contre Moïse et contre Aaron, en disant: Vous avez fait mourir le peuple de l'Eternel.
Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
42 Et il arriva comme l'assemblée s'amassait contre Moïse et contre Aaron, qu'ils regardèrent vers le Tabernacle d'assignation, et voici la nuée le couvrit, et la gloire de l'Eternel apparut.
Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
43 Moïse donc et Aaron vinrent devant le Tabernacle d'assignation.
Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
44 Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
45 Otez-vous du milieu de cette assemblée, et je les consumerai en un moment. Alors ils se prosternèrent le visage contre terre.
“Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
46 Puis Moïse dit à Aaron: Prends l'encensoir, et mets-y du feu de dessus l'autel, mets-y aussi du parfum, et va promptement à l'assemblée, et fais propitiation pour eux; car une grande colère est partie de devant l'Eternel; la plaie est commencée.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
47 Et Aaron prit l'encensoir, comme Moïse lui avait dit, et il courut au milieu de l'assemblée, et voici la plaie avait déjà commencé sur le peuple. Alors il mit du parfum, et fit propitiation pour le peuple.
Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
48 Et comme il se tenait entre les morts elles vivants, la plaie fut arrêtée.
Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
49 Et il y en eut quatorze mille sept cents qui moururent de cette plaie, outre ceux qui étaient morts pour le fait de Coré.
Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
50 Et Aaron retourna vers Moïse à l'entrée du Tabernacle d'assignation, après que la plaie fut arrêtée.
Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.