< Nombres 15 >

1 Puis l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Parle aux enfants d'Israël, et leur dis: Quand vous serez entrés au pays où vous devez demeurer, lequel je vous donne;
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
3 Et que vous voudrez faire un sacrifice par feu à l'Eternel, un holocauste, ou un [autre] sacrifice, pour s'acquitter de quelque vœu, ou volontairement, ou dans vos fêtes solennelles, pour faire une offrande de bonne odeur à l'Eternel, du gros ou du menu bétail;
kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
4 Celui qui offrira son offrande à l'Eternel, offrira avec elle un gâteau de fleur de farine d'une dixième, pétrie avec la quatrième partie d'un Hin d'huile;
sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
5 Et la quatrième partie d'un Hin de vin pour l'aspersion que tu feras sur l'holocauste, ou sur [quelque autre] sacrifice pour chaque agneau.
Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
6 Que si c'est pour un bélier, tu feras un gâteau de deux dixièmes de fleur de farine, pétrie avec la troisième partie d'un Hin d'huile;
“‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
7 Et la troisième partie d'un Hin de vin pour l'aspersion, que tu offriras en bonne odeur à l'Eternel.
da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
8 Et si tu sacrifies un veau en holocauste, ou [tel autre] sacrifice, pour s'acquitter de quelque vœu important, ou pour faire un sacrifice de prospérités à l'Eternel;
“‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
9 On offrira avec le veau un gâteau de trois dixièmes de fleur de farine, pétrie avec la moitié d'un Hin d'huile.
sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
10 Et tu offriras la moitié d'un Hin de vin pour l'aspersion, en offrande faite par feu de bonne odeur à l'Eternel.
A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
11 On en fera de même pour chaque taureau, chaque bélier, et chaque petit d'entre les brebis et d'entre les chèvres.
Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
12 Selon le nombre que vous en sacrifierez, vous ferez ainsi à chacun, selon leur nombre.
Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
13 Tous ceux qui sont nés au pays feront ces choses de cette manière, en offrant un sacrifice fait par feu en bonne odeur à l'Eternel.
“‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 Que si quelque étranger, ou [quelque autre] parmi vous, qui faisant son séjour avec vous, en vos âges, fait un sacrifice par feu en bonne odeur à l'Eternel, il fera comme vous ferez.
Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
15 Ô assemblée! il y aura une même ordonnance pour vous et pour l'étranger qui fait son séjour [parmi vous], il y aura une même ordonnance perpétuelle en vos âges; il en sera de l'étranger comme de vous en la présence de l'Eternel.
Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
16 Il y aura une même loi et un même droit pour vous et pour l'étranger qui fait son séjour parmi vous.
Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
17 L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Parle aux enfants d'Israël, et leur dis: Quand vous serez entrés au pays où je vous ferai entrer;
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
19 Et que vous mangerez du pain du pays, vous en offrirez à l'Eternel une offrande élevée.
kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
20 Vous offrirez en offrande élevée un gâteau pour les prémices de votre pâte; vous l'offrirez à la façon de l'offrande élevée prise de l'aire.
Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
21 Vous donnerez donc en vos âges à l'Eternel une offrande élevée, prise des prémices de votre pâte.
A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
22 Et lorsque vous aurez péché par erreur, et que vous n'aurez pas fait tous ces commandements que l'Eternel a donnés à Moïse;
“‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
23 Tout ce que l'Eternel vous a commandé par le moyen de Moïse, depuis le jour que l'Eternel a commencé de donner ses commandements, et dans la suite en vos âges;
ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
24 S'il arrive que la chose ait été faite par erreur, sans que l'assemblée l'ait aperçue, toute l'assemblée sacrifiera en holocauste en bonne odeur à l'Eternel, un veau pris du troupeau, avec son gâteau et son aspersion, selon l'ordonnance, et un jeune bouc en offrande pour le péché.
in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
25 Ainsi le Sacrificateur fera propitiation pour toute l'assemblée des enfants d'Israël, et il leur sera pardonné; parce que c'est une chose arrivée par erreur; et ils amèneront devant l'Eternel leur offrande qui doit être un sacrifice fait par feu à l'Eternel, et [l'offrande pour] leur péché, à cause de leur erreur.
Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
26 Alors il sera pardonné à toute l'assemblée des enfants d'Israël, et à l'étranger qui fait son séjour parmi eux, parce que cela est arrivé à tout le peuple par erreur.
Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
27 Que si une personne seule a péché par erreur, elle offrira [en offrande pour] le péché une chèvre d'un an.
“‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
28 Et le Sacrificateur fera propitiation pour la personne qui aura péché par erreur, de ce qu'elle aura péché par erreur devant l'Eternel, [et] faisant propitiation pour elle, il lui sera pardonné.
Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
29 Il y aura une même loi pour celui qui aura fait quelque chose par erreur, tant pour celui qui est né au pays des enfants d'Israël, que pour l'étranger qui fait son séjour parmi eux.
Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
30 Mais quant à celui qui aura péché par fierté, tant celui qui est né au pays, que l'étranger, il a outragé l'Eternel; cette personne-là sera retranchée du milieu de son peuple;
“‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
31 Parce qu'il a méprisé la parole de l'Eternel, et qu'il a enfreint son commandement. Cette personne donc sera certainement retranchée; son iniquité est sur elle.
gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
32 Or les enfants d'Israël étant au désert, trouvèrent un homme qui ramassait du bois le jour du Sabbat.
Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
33 Et ceux qui le trouvèrent ramassant du bois, l'amenèrent à Moïse et à Aaron, et à toute l'assemblée.
Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
34 Et on le mit en garde; car il n'avait pas encore été déclaré ce qu'on lui devait faire.
sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
35 Alors l'Eternel dit à Moïse: On punira de mort cet homme-là, et toute l'assemblée le lapidera hors du camp.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
36 Toute l'assemblée donc le mena hors du camp, et ils le lapidèrent, et il mourut; comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse.
Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
37 Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
38 Parle aux enfants d'Israël, et leur dis: Qu'ils se fassent d'âge en âge des bandes aux pans de leurs vêtements, et qu'ils mettent sur les bandes des pans [de leurs vêtements] un cordon de couleur de pourpre.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
39 Ce cordon sera sur la bande, et en le voyant il vous souviendra de tous les commandements de l'Eternel, afin que vous les fassiez, et que vous ne suiviez point les pensées de votre cœur, ni les désirs de vos yeux, en suivant lesquels vous paillardez.
Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
40 Afin que vous vous souveniez de tous mes commandements, et que vous les fassiez, et que vous soyez saints à votre Dieu.
Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
41 Je suis l'Eternel votre Dieu, qui vous ai retirés du pays d'Egypte, pour être votre Dieu; je suis l'Eternel votre Dieu.
Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< Nombres 15 >