< Matthieu 27 >
1 Puis quand le matin fut venu, tous les principaux Sacrificateurs et les Anciens du peuple tinrent conseil contre Jésus pour le faire mourir.
Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
2 Et l'ayant lié, ils l'amenèrent et le livrèrent à Ponce Pilate, qui était le Gouverneur.
Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
3 Alors Judas qui l'avait trahi, voyant qu'il était condamné, se repentit, et reporta les trente pièces d'argent aux principaux Sacrificateurs et aux Anciens,
Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
4 En leur disant: j'ai péché en trahissant le sang innocent; mais ils lui dirent: que nous importe? tu y aviseras.
yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
5 Et après avoir jeté les pièces d'argent dans le Temple, il se retira, et s'en étant allé il s'étrangla.
Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
6 Mais les principaux Sacrificateurs ayant pris les pièces d'argent, dirent: il n'est pas permis de les mettre dans le trésor; car c'est un prix de sang.
Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
7 Et après qu'ils eurent consulté entre eux, ils en achetèrent le champ d'un potier, pour la sépulture des étrangers.
Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
8 C'est pourquoi ce champ-là a été appelé jusqu'à aujourd'hui, le champ du sang.
Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
9 Alors fut accompli ce dont il avait été parlé par Jérémie le Prophète, disant: et ils ont pris trente pièces d'argent, le prix de celui qui a été apprécié, lequel ceux d'entre les enfants d'Israël ont apprécié;
Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
10 Et ils les ont données pour en acheter le champ d'un potier, selon ce que le Seigneur m'avait ordonné.
suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 Or Jésus fut présenté devant le Gouverneur, et le Gouverneur l'interrogea, disant: es-tu le Roi des Juifs? Jésus lui répondit: tu le dis.
Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
12 Et étant accusé par les principaux Sacrificateurs et les Anciens, il ne répondait rien.
Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
13 Alors Pilate lui dit: n'entends-tu pas combien ils portent de témoignages contre toi?
Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
14 Mais il ne lui répondit pas un mot sur quoi que ce fût; de sorte que le Gouverneur s'en étonnait extrêmement.
Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
15 Or le Gouverneur avait accoutumé de relâcher au peuple [le jour de] la Fête un prisonnier, quel que ce fût qu'on demandât.
To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
16 Et il y avait alors un prisonnier fameux, nommé Barabbas.
A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
17 Quand donc ils furent assemblés, Pilate leur dit: lequel voulez-vous que je vous relâche? Barabbas, ou Jésus qu'on appelle Christ?
To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
18 Car il savait bien qu'ils l'avaient livré par envie.
Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
19 Et comme il était assis au siége judicial, sa femme envoya lui dire: n'entre point dans l'affaire de ce juste, car j'ai aujourd'hui beaucoup souffert à son sujet en songeant.
Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
20 Et les principaux Sacrificateurs et les Anciens persuadèrent à la multitude du peuple de demander Barabbas, et de faire périr Jésus.
A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
21 Et le Gouverneur prenant la parole leur dit: Lequel des deux voulez-vous que je vous relâche? Ils dirent: Barabbas.
Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
22 Pilate leur dit: que ferai-je donc de Jésus qu'on appelle Christ? Ils lui dirent tous: qu 'il soit crucifié!
Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
23 Et le Gouverneur leur dit: mais quel mal a-t-il fait? et ils crièrent encore plus fort, en disant: qu'il soit crucifié!
Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
24 Alors Pilate voyant qu'il ne gagnait rien, mais que le tumulte s'augmentait, prit de l'eau, et lava ses mains devant le peuple, en disant: je suis innocent du sang de ce juste, vous y penserez.
Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
25 Et tout le peuple répondant, dit: Que son sang soit sur nous, et sur nos enfants!
Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
26 Alors il leur relâcha Barabbas; et après avoir fait fouetter Jésus, il le leur livra pour être crucifié.
Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
27 Et les soldats du Gouverneur amenèrent Jésus au Prétoire, et assemblèrent devant lui toute la cohorte.
Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
28 Et après l'avoir dépouillé, ils mirent sur lui un manteau d'écarlate.
Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
29 Et ayant fait une couronne d'épines entrelacées, ils la mirent sur sa tête, avec un roseau dans sa main droite; puis s'agenouillant devant lui, ils se moquaient de lui, en disant: nous te saluons, Roi des Juifs!
Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
30 Et après avoir craché contre lui, ils prirent le roseau, et ils en frappaient sa tête.
Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
31 Et après s'être moqués de lui, ils lui ôtèrent le manteau, et le vêtirent de ses vêtements, et l'amenèrent pour le crucifier.
Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
32 Et comme ils sortaient, ils rencontrèrent un Cyrénéen, nommé Simon, lequel ils contraignirent de porter la croix de Jésus.
Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
33 Et étant arrivés au lieu appelé Golgotha, c'est-à-dire, le lieu du Crâne,
Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
34 Ils lui donnèrent à boire du vinaigre mêlé avec du fiel; mais quand il en eut goûté, il n'en voulut point boire.
Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
35 Et après l'avoir crucifié, ils partagèrent ses vêtements, en les jetant au sort, afin que ce qui avait été dit par un Prophète, fût accompli: ils ont partagé entre eux mes vêtements, et ont jeté ma robe au sort.
Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
36 Puis s'étant assis, ils le gardaient là.
Suka kuma zauna suna kallonsa.
37 Ils mirent aussi au-dessus de sa tête un écriteau, où la cause [de sa condamnation] était marquée en ces mots: CELUI-CI EST JÉSUS LE ROI DES JUIFS.
A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
38 Et deux brigands furent crucifiés avec lui, l'un à sa droite, et l'autre à sa gauche.
An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
39 Et ceux qui passaient par là, lui disaient des outrages, en branlant la tête,
Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
40 Et disant: toi qui détruis le Temple, et qui le rebâtis en trois jours, sauve-toi toi-même; si tu es le Fils de Dieu, descends de la croix.
suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
41 Pareillement aussi les principaux Sacrificateurs avec les Scribes et les Anciens, se moquant, disaient:
Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
42 Il a sauvé les autres, il ne se peut sauver lui-même: s'il est le Roi d'Israël, qu'il descende maintenant de la croix, et nous croirons en lui.
“Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
43 Il se confie en Dieu; [mais] si [Dieu] l'aime, qu'il le délivre maintenant, car il a dit: je suis le Fils de Dieu.
Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
44 Les brigands aussi qui étaient crucifiés avec lui, lui reprochaient la même chose.
Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
45 Or depuis six heures il y eut des ténèbres sur tout le pays, jusqu'à neuf heures.
To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
46 Et environ les neuf heures Jésus s'écria à haute voix, en disant: Eli, Eli, lamma sabachthani? c'est-à-dire, Mon Dieu! mon Dieu! pourquoi m'as-tu abandonné?
Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
47 Et quelques-uns de ceux qui étaient là présents, ayant entendu cela, disaient: il appelle Elie.
Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
48 Et aussitôt un d'entre eux courut, et prit une éponge, et l'ayant remplie de vinaigre, la mit au bout d'un roseau, et lui en donna à boire.
Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
49 Mais les autres disaient: laisse, voyons si Elie viendra le sauver.
Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
50 Alors Jésus ayant crié encore à haute voix, rendit l'esprit.
Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
51 Et voici, le voile du Temple se déchira en deux, depuis le haut jusqu'en bas; et la terre trembla, et les pierres se fendirent.
Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
52 Et les sépulcres s'ouvrirent, et plusieurs corps des Saints, qui étaient morts ressuscitèrent.
Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
53 Et étant sortis des sépulcres après sa résurrection, ils entrèrent dans la sainte Citée, et se montrèrent à plusieurs.
Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
54 Or le Centenier, et ceux qui avec lui gardaient Jésus, ayant vu le tremblement de terre, et tout ce qui venait d'arriver, eurent une fort grande peur, et dirent: certainement celui-ci était le Fils de Dieu.
Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
55 Il y avait là aussi plusieurs femmes qui regardaient de loin, et qui avaient suivi Jésus depuis la Galilée, en le servant.
Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
56 Entre lesquelles étaient Marie-Magdeleine; et Marie mère de Jacques et de Joses; et la mère des fils de Zébédée.
A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
57 Et le soir étant venu, un homme riche d'Arimathée, nommé Joseph, qui même avait été Disciple de Jésus,
Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
58 Vint à Pilate, et demanda le corps de Jésus; et en même temps Pilate commanda que le corps fût rendu.
Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
59 Ainsi Joseph prit le corps, et l'enveloppa d'un linceul net;
Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
60 Et le mit dans son sépulcre neuf, qu'il avait taillé dans le roc; et après avoir roulé une grande pierre à l'entrée du sépulcre, il s'en alla.
sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
61 Et là étaient Marie-Magdeleine et l'autre Marie, assises vis-à-vis du sépulcre.
Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
62 Or le lendemain, qui est après la préparation [du Sabbat], les principaux Sacrificateurs et les Pharisiens s'assemblèrent vers Pilate,
Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
63 Et lui dirent: Seigneur! il nous souvient que ce séducteur disait, quand il était encore en vie: dans trois jours je ressusciterai.
Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
64 Commande donc que le sépulcre soit gardé sûrement jusques au troisième jour; de peur que ses Disciples ne viennent de nuit, et ne le dérobent, et qu'ils ne disent au peuple: il est ressuscité des morts; car cette dernière imposture serait pire que la première.
Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
65 Mais Pilate leur dit: vous avez la garde; allez, et assurez-le comme vous l'entendrez.
Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
66 Ils s'en allèrent donc, et assurèrent le sépulcre, scellant la pierre, et y mettant des gardes.
Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.