< Matthieu 17 >
1 Et six jours après, Jésus prit Pierre, et Jacques, et Jean son frère, et les mena à l'écart sur une haute montagne.
Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus da Yakubu, da Yahaya dan'uwansa, ya kai su kan wani dutse mai tsawo su kadai.
2 Et il fut transfiguré en leur présence et son visage resplendit comme le soleil; et ses vêtements devinrent blancs comme la lumière.
Kamanninsa ya canja a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, kuma rigunansa suka yi kyalli fal.
3 Et voici, ils virent Moïse et Elie, qui s'entretenaient avec lui.
Sai ga Musa da Iliya sun bayyana garesu suna magana da shi.
4 Alors Pierre prenant la parole, dit à Jésus: Seigneur, il est bon que nous soyons ici; faisons-y, si tu le veux, trois tentes, une pour toi, une pour Moïse, et une pour Elie.
Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke a wurin nan. In kana so, zan yi bukkoki uku daya dominka, daya domin Musa, daya domin Iliya.”
5 Et comme il parlait encore, voici une nuée resplendissante qui les couvrit de son ombre; puis voilà une voix qui vint de la nuée, disant: celui-ci est mon Fils bien-aimé, en qui j'ai pris mon bon plaisir; écoutez-le.
Sa'adda yake cikin magana, sai, girgije mai haske ya rufe su, sai murya daga girgijen, tana cewa, “Wannan kaunattacen Dana ne, shi ne wanda yake faranta mani zuciya. Ku saurare shi.”
6 Ce que les Disciples ayant ouï, ils tombèrent le visage contre terre, et eurent une très grande peur.
Da almajiran suka ji haka, suka fadi da fuskokinsu a kasa, saboda sun tsorata.
7 Mais Jésus s'approchant les toucha, en leur disant: levez-vous, et n'ayez point de peur.
Sai Yesu ya zo ya taba su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
8 Et eux levant leurs yeux, ne virent personne, que Jésus tout seul.
Amma da suka daga kai ba su ga kowa ba sai Yesu kadai.
9 Et comme ils descendaient de la montagne, Jésus leur commanda, en disant: ne dites à personne la vision, jusqu'à ce que le Fils de l'homme soit ressuscité des morts.
Yayin da suke saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su, ya ce, “Kada ku fadawa kowa wannan wahayin, sai Dan Mutum ya tashi daga matattu.”
10 Et ses Disciples l'interrogèrent, en disant: pourquoi donc les Scribes disent-ils qu'il faut qu'Elie vienne premièrement?
Almajiransa suka tambaye shi, suka ce, “Don me marubuta ke cewa lallai ne Iliya ya fara zuwa?”
11 Et Jésus répondant dit: il est vrai qu'Elie viendra premièrement, et qu'il rétablira toutes choses.
Yesu ya amsa ya ce, “Hakika, Iliya zai zo ya maido da dukan abubuwa.
12 Mais je vous dis qu'Elie est déjà venu, et ils ne l'ont point connu; mais ils lui ont fait tout ce qu'ils ont voulu; ainsi le Fils de l'homme doit souffrir aussi de leur part.
Amma ina gaya maku, Iliya ya riga ya zo, amma ba su gane shi ba. A maimakon haka, suka yi masa abin da suka ga dama. Ta irin wanan hanya, Dan Mutum kuma zai sha wuya a hannunsu.
13 Alors les Disciples comprirent que c'était de Jean Baptiste qu'il leur avait parlé.
Sa'annan almajiransa suka fahimci cewa yana yi masu magana a kan Yahaya mai Baftisma ne.
14 Et quand ils furent venus vers les troupes, un homme s'approcha, et se mit à genoux devant lui,
Da suka iso wurin taron, wani mutum ya zo gunsa, ya durkusa a gaban sa, ya ce,
15 Et lui dit: Seigneur! aie pitié de mon fils, qui est lunatique, et misérablement affligé; car il tombe souvent dans le feu, et souvent dans l'eau.
“Ubangiji, ka ji tausayin yarona, domin yana da farfadiya, kuma yana shan wuya kwarai, domin sau da yawa yana fadawa cikin wuta ko ruwa.
16 Et je l'ai présenté à tes Disciples; mais ils ne l'ont pu guérir.
Na kawo shi wurin almajiran ka, amma ba su iya su warkar da shi ba.”
17 Et Jésus répondant, dit: Ô race incrédule, et perverse, jusques à quand serai-je avec vous? jusques à quand vous supporterai-je? amenez-le-moi ici.
Yesu ya amsa ya ce, “Marasa bangaskiya da karkataccen zamani, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan jure da ku? Ku kawo shi nan a wurina.”
18 Et Jésus censura fortement le démon, qui sortit hors de cet enfant, et à l'heure même l'enfant fut guéri.
Yesu ya tsauta masa, sai aljanin ya fita daga cikinsa. Yaron ya warke nan take.
19 Alors les Disciples vinrent en particulier à Jésus, et lui dirent: pourquoi ne l'avons-nous pu jeter dehors?
Sai almajiran suka zo wurin Yesu a asirce suka ce, “Me ya sa muka kasa fitar da shi?”
20 Et Jésus leur répondit: c'est à cause de votre incrédulité: car en vérité je vous dis, que si vous aviez de la foi, aussi gros qu'un grain de semence de moutarde, vous diriez à cette montagne: transporte-toi d'ici là, et elle s'y transporterait; et rien ne vous serait impossible.
Yesu ya ce masu, “Saboda karancin bangaskiyarku. Domin hakika, ina gaya maku, in kuna da bangaskiya ko da kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan dutse, 'Matsa daga nan ka koma can,' zai kuwa matsa kuma ba abin da zai gagare ku.
21 Mais cette sorte [de démons] ne sort que par la prière et par le jeûne.
[Irin wannan aljanin bashi fita sai tare da addu'a da azumi].
22 Et comme ils se trouvaient en Galilée, Jésus leur dit: il arrivera que le Fils de l'homme sera livré entre les mains des hommes;
Suna zaune a Galili, Yesu ya ce wa almajiransa, “Za a bada Dan Mutum ga hannun mutane.
23 Et qu'ils le feront mourir, mais le troisième jour il ressuscitera. Et [les Disciples] en furent fort attristés.
Kuma za su kashe shi, a rana ta uku zai tashi.” Sai almajiransa suka yi bakin ciki kwarai.
24 Et lorsqu'ils furent venus à Capernaüm, ceux qui recevaient les didrachmes s'adressèrent à Pierre et lui dirent: votre Maître ne paye-t-il pas les didrachmes?
Da suka iso Kafarnahum, mutane masu karbar haraji na rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku na ba da rabin shekel na haraji?”
25 Il dit: oui. Et quand il fut entré dans la maison, Jésus le prévint, en lui disant: qu'est-ce qu'il t'en semble, Simon? Les Rois de la terre, de qui prennent-ils des tributs, ou des impôts? est-ce de leurs enfants, ou des étrangers?
Sai ya ce, “I.” Amma da Bitrus ya shiga cikin gida, Yesu ya fara magana da shi yace, “Menene tunaninka Saminu? Sarakunan duniya, daga wurin wa suke karbar haraji ko kudin fito? Daga talakawansu ko daga wurin baki?”
26 Pierre dit: des étrangers. Jésus lui répondit: les enfants en sont donc exempts.
Sai Bitrus ya ce, “Daga wurin baki,” Yesu ya ce masa, “Wato an dauke wa talakawansu biya kenan.
27 Mais afin que nous ne les scandalisions point, va-t'en à la mer, et jette l'hameçon, et prends le premier poisson qui montera; et quand tu lui auras ouvert la bouche, tu y trouveras un statère; prends-le, et le leur donne pour moi et pour toi.
Amma don kada mu sa masu karbar harajin su yi zunubi, ka je teku, ka jefa kugiya, ka cire kifin da ya fara zuwa. Idan ka bude bakinsa, za ka sami shekel. Ka dauke shi ka ba masu karbar harajin nawa da naka.