< Matthieu 11 >

1 Et il arriva que quand Jésus eut achevé de donner ses ordres à ses douze Disciples, il partit de là pour aller enseigner et prêcher dans leurs villes.
Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa gargadi, sai ya bar wannan wuri, ya tafi biranensu domin yayi koyorwa, da wa'azi.
2 Or Jean ayant ouï parler dans la prison des actions de Christ, envoya deux de ses Disciples pour lui dire:
Da Yahaya mai baftisma ya ji daga kurkuku irin ayyukan da Yesu ke yi, sai ya aika sako ta wurin almajiransa.
3 Es-tu celui qui devait venir, ou si nous devons en attendre un autre?
Ya ce masa. “Kai ne mai zuwa”? ko mu sa ido ga wani.
4 Et Jésus répondant, leur dit: allez, et rapportez à Jean les choses que vous entendez, et que vous voyez.
Yesu ya amsa ya ce masu, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da ku ka gani da abin da ku ka ji.
5 Les aveugles recouvrent la vue, les boiteux marchent, les lépreux sont nettoyés, les sourds entendent, les morts sont ressuscités, et l'Evangile est annoncé aux pauvres.
Makafi suna samun ganin gari, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na jin magana kuma, ana tada matattu, mabukata kuma ana ba su bishara.
6 Mais bienheureux est celui qui n'aura point été scandalisé en moi.
Kuma mai albarka ne wanda baya tuntube sabili da ni.
7 Et comme ils s'en allaient, Jésus se mit à dire de Jean aux troupes: qu'êtes-vous allés voir au désert? Un roseau agité du vent?
Bayan wadannan sun tafi, sai Yesu ya fara wa jama'a jawabi game da Yahaya mai baftisma, yana cewa, “Me ake zuwa gani a jeji - ciyawa ce da iska ke busawa?
8 Mais qu'êtes-vous allés voir? Un homme vêtu de précieux vêtements? voici, ceux qui portent des habits précieux, sont dans les maisons des Rois.
Shin menene kuke zuwa gani a jeji - mutum mai sanye da tufafi masu laushi? Hakika, masu sa tufafi masu laushi suna zaune ne a fadar sarakuna.
9 Mais qu'êtes-vous allés voir? Un Prophète? oui, vous dis-je, et plus qu'un Prophète.
Amma me ku ke zuwa gani, annabi? Hakika ina fada maku, fiye ma da annabi.
10 Car il est celui duquel il a été [ainsi] écrit: voici, j'envoie mon messager devant ta face, lequel préparera ton chemin devant toi.
Wannan shine wanda aka rubuta game da shi, 'Duba, ina aika manzona, wanda za ya tafi gabanka domin ya shirya maka hanya inda za ka bi'.
11 En vérité, je vous dis, qu'entre ceux qui sont nés d'une femme, il n'en a été suscité aucun plus grand que Jean Baptiste; toutefois celui qui est le moindre dans le Royaume des cieux, est plus grand que lui.
Ina gaya maku gaskiya, cikin wadanda mata suka haifa, babu mai girma kamar Yahaya mai baftisma. Amma mafi kankanta a mulkin sama ya fi shi girma.
12 Or depuis les jours de Jean Baptiste jusques à maintenant, le Royaume des cieux est forcé, et les violents le ravissent.
Tun daga kwanakin Yahaya mai baftisma zuwa yanzu, mulkin sama yana shan gwagwarmaya, masu husuma kuma su kan kwace shi da karfi.
13 Car tous les Prophètes et la Loi jusqu'à Jean ont prophétisé.
Gama dukan annabawa da shari'a sun yi annabci har zuwa lokacin Yahaya.
14 Et si vous voulez recevoir [mes paroles], c'est l'Elie qui devait venir.
kuma in zaku karba, wannan shine Iliya wanda za ya zo.
15 Qui a des oreilles pour ouïr, qu'il entende.
Wanda ke da kunnuwan ji, ya ji.
16 Mais à qui comparerai-je cette génération? Elle est semblable aux petits enfants qui sont assis aux marchés, et qui crient à leurs compagnons,
Da me zan kwatanta wannan zamani? Ya na kamar yara masu wasa a kasuwa, sun zauna suna kiran juna
17 Et leur disent: nous avons joué de la flûte, et vous n'avez point dansé; nous vous avons chanté des airs lugubres, et vous ne vous êtes point lamentés.
suna cewa mun busa maku sarewa baku yi rawa ba, mun yi makoki, baku yi kuka ba.
18 Car Jean est venu ne mangeant ni ne buvant; et ils disent: il a un démon.
Gama Yahaya ya zo, baya cin gurasa ko shan ruwan inabi, sai aka ce, “Yana da aljannu”.
19 Le Fils de l'homme est venu mangeant et buvant; et ils disent: voilà un mangeur et un buveur, un ami des péagers et des gens de mauvaise vie; mais la sagesse a été justifiée par ses enfants.
Dan mutum ya zo yana ci yana sha, sai aka ce, 'Duba, ga mai hadama, mashayi kuma, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!' Amma hikima, ta wurin aikin ta ake tabbatar da ita.
20 Alors il commença à reprocher aux villes où il avait fait beaucoup de miracles, qu'elles ne s'étaient point repenties, [en leur disant]:
Sannan Yesu ya fara tsautawa biranen nan inda ya yi yawancin ayukansa, domin ba su tuba ba.
21 Malheur à toi, Corazin! malheur à toi, Bethsaïda! car si les miracles qui ont été faits au milieu de vous, eussent été faits dans Tyr et dans Sidon, il y a longtemps qu'elles se seraient repenties avec le sac et la cendre.
“Kaiton ki Korasinu, kaiton ki Batsaida! In da an yi irin ayuka masu ban mamaki a Taya da Sidon! Yadda aka yi a cikinku, da tuni sun tuba suna sanye da tsumma da yafa toka.
22 C'est pourquoi je vous dis que Tyr et Sidon seront traitées moins rigoureusement que vous, au jour du jugement.
Amma zai zama da sauki a kan Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku.
23 Et toi Capernaüm, qui as été élevée jusques au ciel, tu seras abaissée jusque dans l'enfer; car si les miracles qui ont été faits au milieu de toi, eussent été faits dans Sodome, elle subsisterait encore. (Hadēs g86)
Ke kafarnahum, kina tsammani za a daukaka ki har zuwa sama? A'a za a saukar da ke kasa zuwa hades. Gama in da an yi irin al'ajiban da aka yi a cikin ki a Sodom, da tana nan har yanzu. (Hadēs g86)
24 C'est pourquoi je vous dis, que ceux de Sodome seront traités moins rigoureusement que toi, au jour du jugement.
Amma ina ce maku, za a saukaka wa Sodom a ranar shari'a fiye da ku.”
25 En ce temps-là Jésus prenant la parole dit: je te célèbre, ô mon Père! Seigneur du ciel et de la terre, de ce que tu as caché ces choses aux sages et aux intelligents, et que tu les as révélées aux petits enfants.
A wannan lokaci Yesu ya ce, “Ina yabon ka, ya Uba, Ubangijin sama da kasa, domin ka boye wa masu hikima da fahimta wadannan abubuwa, ka bayyana wa marasa sani, kamar kananan yara.
26 Il est ainsi, ô mon Père! parce que telle a été ta bonne volonté.
I, ya Uba gama wannan shine ya yi daidai a gare ka.
27 Toutes choses m'ont été accordées par mon Père! mais personne ne connaît le Fils, que le Père; et personne ne connaît le Père que le Fils, et celui à qui le Fils l'aura voulu révéler.
An mallaka mani dukan abu daga wurin Ubana. Sannan babu wanda ya san Dan, sai Uban, babu kuma wanda ya san Uban, sai Dan, da duk wanda ya so ya bayyana masa.
28 Venez à moi vous tous qui êtes fatigués et chargés, et je vous soulagerai.
Ku zo gare ni, dukanku masu wahala da fama da nauyin kaya, ni kuma zan ba ku hutawa.
29 Chargez mon joug sur vous, et apprenez de moi parce que je suis doux et humble de cœur; et vous trouverez le repos de vos âmes.
Ku dauki karkiya ta ku koya daga gare ni, gama ni mai tawali'u ne da saukin hali a zuciya, sannan zaku sami hutawa ga rayukanku.
30 Car mon joug est aisé, et mon fardeau est léger.
Gama karkiyata mai sauki ce, kaya na kuma ba shi da nauyi.”

< Matthieu 11 >