< Marc 6 >

1 Puis il partit de là, et vint en son pays; et ses Disciples le suivirent.
Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
2 Et le jour du Sabbat étant venu, il se mit à enseigner dans la Synagogue; et beaucoup de ceux qui l'entendaient, étaient dans l'étonnement, et ils disaient: d'où viennent ces choses à celui-ci? et quelle est cette sagesse qui lui est donnée; et que même de tels prodiges se fassent par ses mains?
Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
3 Celui-ci n'est-il pas charpentier? fils de Marie, frère de Jacques, et de Joses, et de Jude, et de Simon? et ses sœurs ne sont-elles pas ici parmi nous? et ils étaient scandalisés à cause de lui.
Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
4 Mais Jésus leur dit: un Prophète n'est sans honneur que dans son pays, et parmi ses parents et ceux de sa famille.
Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
5 Et il ne put faire là aucun miracle, sinon qu'il guérit quelque peu de malades, en leur imposant les mains.
Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
6 Et il s'étonnait de leur incrédulité, et parcourait les villages d'alentour, en enseignant.
Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
7 Alors il appela les douze, et commença à les envoyer deux à deux, et leur donna puissance sur les esprits immondes.
Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
8 Et il leur commanda de ne rien prendre pour le chemin, qu'un seul bâton, [et de ne porter] ni sac, ni pain, ni monnaie dans leur ceinture;
ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
9 Mais d'être chaussés de souliers, et de ne porter point deux robes.
sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
10 Il leur disait aussi: partout où vous entrerez dans une maison, demeurez-y jusqu'à ce que vous partiez de là.
Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
11 Et tous ceux qui ne vous recevront point, et ne vous écouteront point, en partant de là, secouez la poussière de vos pieds, pour être un témoignage contre eux. En vérité je vous dis, que ceux de Sodome et de Gomorrhe seront traités moins rigoureusement au jour du jugement que cette ville-là.
Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
12 Etant donc partis, ils prêchèrent qu'on s'amendât.
Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
13 Et ils chassèrent plusieurs démons hors [des possédés], et oignirent d'huile plusieurs malades, et les guérirent.
Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
14 Or le Roi Hérode en ouït parler, car le nom [de Jésus] était devenu fort célèbre, et il dit: Ce Jean qui baptisait, est ressuscité des morts; c'est pourquoi la vertu de faire des miracles agit puissamment en lui.
Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
15 Les autres disaient: c'est Elie; et les autres disaient: c'est un Prophète, ou comme un des Prophètes.
Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
16 Quand donc Hérode eut appris cela, il dit: c'est Jean que j'ai fait décapiter, il est ressuscité des morts.
Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
17 Car Hérode avait envoyé prendre Jean, et l'avait fait lier dans une prison, à cause d'Hérodias femme de Philippe son frère, parce qu'il l'avait prise en mariage.
Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
18 Car Jean disait à Hérode: il ne t'est pas permis d'avoir la femme de ton frère.
Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
19 C'est pourquoi Hérodias lui en voulait, et désirait de le faire mourir, mais elle ne pouvait.
Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
20 Car Hérode craignait Jean, sachant que c'était un homme juste et saint, et il avait du respect pour lui, et lorsqu'il l'avait entendu, il faisait beaucoup de choses [que Jean avait dit de faire], car il l’écoutait volontiers.
Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
21 Mais un jour étant venu à propos, qu'Hérode faisait le festin du jour de sa naissance aux grands Seigneurs, et aux Capitaines, et aux Principaux de la Galilée,
Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
22 La fille d'Hérodias y entra, et dansa, et ayant plu à Hérode, et à ceux qui étaient à table avec lui, le Roi dit à la jeune fille: demande-moi ce que tu voudras, et je te le donnerai.
Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
23 Et il lui jura, disant: tout ce que tu me demanderas, je te le donnerai, jusqu'à la moitié de mon Royaume.
Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
24 Et elle étant sortie, dit à sa mère: qu'est-ce que je demanderai? Et [sa mère lui] dit: la tête de Jean Baptiste.
Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
25 Puis étant aussitôt rentrée avec empressement vers le Roi, elle lui fit sa demande, en disant: je voudrais qu'incessamment tu me donnasses dans un plat la tête de Jean Baptiste.
Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
26 Et le Roi en fut très marri, mais il ne voulut pas la refuser à cause du serment, et de ceux qui étaient à table avec lui:
Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
27 Et il envoya incontinent un de ses gardes, et lui commanda d'apporter la tête de Jean: [le garde] y alla, et décapita [Jean] dans la prison;
Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
28 Et apporta sa tête dans un plat, et la donna à la jeune fille, et la jeune fille la donna à sa mère.
Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
29 Ce que les disciples [de Jean] ayant appris, ils vinrent et emportèrent son corps, et le mirent dans un sépulcre.
Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
30 Or les Apôtres se rassemblèrent vers Jésus, et lui racontèrent tout ce qu'ils avaient fait, et enseigné.
Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
31 Et il leur dit: venez-vous-en à l'écart dans un lieu retiré, et vous reposez un peu; car il y avait beaucoup de gens qui allaient et qui venaient, de sorte qu'ils n'avaient pas même le loisir de manger.
Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
32 Ils s'en allèrent donc dans une nacelle en un lieu retiré, pour y être en particulier.
Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
33 Mais le peuple vit qu'ils s'en allaient, et plusieurs l'ayant reconnu, y accoururent à pied de toutes les villes, et y arrivèrent avant eux, et s'assemblèrent auprès de lui.
Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
34 Et Jésus étant sorti, vit là de grandes troupes, et il fut ému de compassion envers elles, de ce qu'elles étaient comme des brebis qui n'ont point de pasteur; et il se mit à leur enseigner plusieurs choses.
Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
35 Et comme il était déjà tard, ses Disciples s'approchèrent de lui, en disant: ce lieu est désert, et il est déjà tard.
Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
36 Donne-leur congé, afin qu'ils s'en aillent aux villages et aux bourgades d'alentour, et qu'ils achètent des pains pour eux; car ils n'ont rien à manger.
Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
37 Et il leur répondit, et dit: donnez-leur vous-mêmes à manger. Et ils lui dirent: irions-nous acheter pour deux cents deniers de pain, afin de leur donner à manger?
Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
38 Et il leur dit: combien avez-vous de pains? allez et regardez. Et après l'avoir su, ils dirent: cinq, et deux poissons.
Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
39 Alors il leur commanda de les faire tous asseoir par troupes sur l'herbe verte.
Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
40 Et ils s'assirent par troupes, les unes de cent, et les autres de cinquante personnes.
Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
41 Et quand il eut pris les cinq pains et les deux poissons, regardant vers le ciel, il bénit [Dieu], et rompit les pains, puis il les donna à ses Disciples, afin qu'ils les missent devant eux, et il partagea à tous les deux poissons.
Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
42 Et ils en mangèrent tous, et furent rassasiés.
Dukansu suka ci suka koshi.
43 Et on emporta des pièces de pain douze corbeilles pleines, et quelques restes des poissons.
Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
44 Or ceux qui avaient mangé des pains étaient environ cinq mille hommes.
Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
45 Et aussitôt après il obligea ses Disciples de monter sur la nacelle, et d'aller devant lui au delà de la [mer] vers Bethsaïda, pendant qu'il donnerait congé aux troupes.
Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
46 Et quand il leur eut donné congé, il s'en alla sur la montagne pour prier.
Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
47 Et le soir étant venu, la nacelle était au milieu de la mer, et lui seul était à terre.
Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
48 Et il vit qu'ils avaient grande peine à ramer, parce que le vent leur était contraire; et environ la quatrième veille de la nuit, il alla vers eux marchant sur la mer, et il les voulait devancer.
Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
49 Mais quand ils le virent marchant sur la mer, ils crurent que ce fût un fantôme, et ils s'écrièrent.
Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
50 Car ils le virent tous, et ils furent troublés; mais il leur parla aussitôt, et leur dit: rassurez-vous, c'est moi; n'ayez point de peur.
gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
51 Et il monta vers eux dans la nacelle, et le vent cessa; ce qui augmenta beaucoup leur étonnement et leur admiration.
Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
52 Car ils n'avaient pas bien fait réflexion au [miracle des] pains; à cause que leur cœur était stupide.
Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
53 Et quand ils furent passés au delà de la mer, ils arrivèrent en la contrée de Génézareth, où ils abordèrent.
Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
54 Et après qu'ils furent sortis de la nacelle, ceux du lieu le reconnurent d'abord.
Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
55 Et ils coururent çà et là par toute la contrée d'alentour, et se mirent à lui apporter de tous côtés les malades dans de petits lits, là où ils entendaient dire qu'il était.
Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
56 Et partout où il était entré dans les bourgs, ou dans les villes, ou dans les villages, ils mettaient les malades dans les marchés, et ils le priaient de permettre qu'au moins ils pussent toucher le bord de sa robe; et tous ceux qui le touchaient, étaient guéris.
Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.

< Marc 6 >