< Marc 15 >
1 Et d'abord au matin les principaux Sacrificateurs avec les Anciens et les Scribes, et tout le Consistoire, ayant tenu conseil, firent lier Jésus, et l'emmenèrent, et le livrèrent à Pilate.
Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
2 Et Pilate l'interrogea, disant: es-tu le Roi des Juifs? Et [Jésus] répondant lui dit: tu le dis.
Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
3 Or les principaux Sacrificateurs l'accusaient de plusieurs choses, mais il ne répondit rien.
Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
4 Et Pilate l'interrogea encore, disant: ne réponds-tu rien? vois combien de choses ils déposent contre toi.
Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
5 Mais Jésus ne répondit rien non plus; de sorte que Pilate s'en étonnait.
Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
6 Or il leur relâchait à la Fête un prisonnier, lequel que ce fût qu'ils demandassent.
A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
7 Et il y en avait un, nommé Barabbas, qui était prisonnier avec ses complices pour une sédition, dans laquelle ils avaient commis un meurtre.
A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
8 Et le peuple criant tout haut, se mit à demander [à Pilate qu'il fît] comme il leur avait toujours fait.
Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
9 Mais Pilate leur répondit, en disant: voulez-vous que je vous relâche le Roi des Juifs?
Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
10 (Car il savait bien que les principaux Sacrificateurs l'avaient livré par envie.)
Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
11 Mais les principaux Sacrificateurs excitèrent le peuple à demander que plutôt il relâchât Barabbas.
Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
12 Et Pilate répondant, leur dit encore: que voulez-vous donc que je fasse de celui que vous appelez Roi des Juifs?
Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
13 Et ils s'écrièrent encore: crucifie-le.
sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
14 Alors Pilate leur dit: mais quel mal a-t-il fait? et ils s'écrièrent encore plus fort: crucifie-le.
Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
15 Pilate donc voulant contenter le peuple, leur relâcha Barabbas; et après avoir fait fouetter Jésus, il le livra pour être crucifié.
Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
16 Alors les soldats l'emmenèrent dans la cour, qui est le Prétoire, et toute la cohorte s'étant là assemblée,
Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
17 Ils le vêtirent d'une robe de pourpre, et ayant fait une couronne d'épines entrelacées l'une dans l'autre, ils la lui mirent sur la tête;
Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
18 Puis ils commencèrent à le saluer, [en lui disant]: nous te saluons, Roi des Juifs;
Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
19 Et ils lui frappaient la tête avec un roseau, et crachaient contre lui; et se mettant à genoux, ils se prosternaient devant lui.
Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
20 Et après s'être [ainsi] moqués de lui, ils le dépouillèrent de la robe de pourpre, et le revêtirent de ses habits, et l'emmenèrent dehors pour le crucifier.
Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
21 Et ils contraignirent un certain [homme, nommé] Simon, Cyrénéen, père d'Alexandre et de Rufus, qui passait [par là], revenant des champs, de porter sa croix.
Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
22 Et ils le menèrent au lieu [appelé] Golgotha, c'est-à-dire, le lieu du Crâne.
Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
23 Et ils lui donnèrent à boire du vin mixtionné avec de la myrrhe; mais il ne le prit point.
Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
24 Et quand ils l'eurent crucifié, ils partagèrent ses vêtements, en les jetant au sort pour savoir ce que chacun en aurait.
Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
25 Or il était trois heures quand ils le crucifièrent.
A sa'a ta uku aka giciye shi.
26 Et l'écriteau contenant la cause de sa condamnation était: LE ROI DES JUIFS.
Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
27 Ils crucifièrent aussi avec lui deux brigands, l'un à sa main droite, et l'autre à sa gauche.
Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
28 Et ainsi fut accomplie l'Ecriture, qui dit: Et il a été mis au rang des malfaiteurs.
Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
29 Et ceux qui passaient près de là lui disaient des outrages, branlant la tête, et disant: Hé! toi, qui détruis le Temple, et qui le rebâtis en trois jours,
suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
30 Sauve-toi toi-même, et descends de la croix.
ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
31 Les principaux Sacrificateurs se moquant aussi avec les Scribes disaient entre eux: il a sauvé les autres, il ne peut se sauver lui-même.
Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
32 Que le Christ, le Roi d’Israël descende maintenant de la croix, afin que nous le voyions et que nous croyions! Ceux aussi qui étaient crucifiés avec lui, lui disaient des outrages.
Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
33 Mais quand il fut six heures, il y eut des ténèbres sur tout le pays jusqu'à neuf heures.
sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
34 Et à neuf heures Jésus cria à haute voix, disant: Eloï, Eloï, lamma sabachthani? c'est-à-dire: Mon Dieu! Mon Dieu! pourquoi m'as-tu abandonné?
A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
35 Ce que quelques-uns de ceux qui étaient là présents, ayant entendu, ils dirent: voilà, il appelle Elie.
Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
36 Et quelqu'un accourut, qui remplit une éponge de vinaigre, et qui l'ayant mise au bout d'un roseau, lui en donna à boire, en disant: laissez, voyons si Elie viendra pour l'ôter de la croix.
Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
37 Et Jésus ayant jeté un grand cri, rendit l'esprit.
Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
38 Et le voile du Temple se déchira en deux, depuis le haut jusqu'en bas.
Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
39 Et le Centenier qui était là vis-à-vis de lui, voyant qu'il avait rendu l'esprit en criant ainsi, dit: certainement cet homme était Fils de Dieu.
Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
40 Il y avait là aussi des femmes qui regardaient de loin, entre lesquelles étaient Marie-Magdeleine, et Marie [mère] de Jacques le mineur, et de Joses, et Salomé.
Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
41 Qui lorsqu'il était en Galilée, l'avaient suivi, et l'avaient servi; [il y avait là] aussi plusieurs autres femmes qui étaient montées avec lui à Jérusalem.
Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
42 Et le soir étant déjà venu, parce que c'était la Préparation qui est avant le Sabbat;
Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
43 Joseph d'Arimathée, Conseiller honorable, qui attendait aussi le Règne de Dieu, s'étant enhardi, vint à Pilate, et [lui] demanda le corps de Jésus.
Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
44 Et Pilate s'étonna qu'il fût déjà mort; et ayant appelé le Centenier, il lui demanda s'il y avait longtemps qu'il était mort.
Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
45 Ce qu'ayant appris du Centenier, il donna le corps à Joseph.
Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
46 Et [Joseph] ayant acheté un linceul, le descendit de la croix, et l'enveloppa du linceul, et le mit dans un sépulcre qui était taillé dans le roc, puis il roula une pierre sur l'entrée du sépulcre.
Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
47 Et Marie-Magdeleine, et Marie [mère] de Joses regardaient où on le mettait.
Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.