< Marc 13 >

1 Et comme il se retirait du Temple, un de ses Disciples lui dit: Maître, regarde quelles pierres et quels bâtiments.
Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
2 Et Jésus répondant lui dit: vois-tu ces grands bâtiments? il n'y sera point laissé pierre sur pierre qui ne soit démolie.
Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
3 Et comme il se fut assis au mont des oliviers vis-à-vis du Temple, Pierre et Jacques, Jean et André, l’interrogèrent en particulier,
Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
4 [Disant]: dis-nous quand ces choses arriveront, et quel signe il y aura quand toutes ces choses devront s'accomplir.
“Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
5 Et Jésus leur répondant, se mit à leur dire: prenez garde que quelqu'un ne vous séduise.
Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
6 Car plusieurs viendront en mon Nom, disant: c'est moi [qui suis le Christ]. Et ils en séduiront plusieurs.
Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
7 Or quand vous entendrez des guerres, et des bruits de guerres, ne soyez point troublés; parce qu'il faut que ces choses arrivent; mais ce ne sera pas encore la fin.
Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
8 Car une nation s'élèvera contre une autre nation, et un Royaume contre un autre Royaume; et il y aura des tremblements de terre de lieu en lieu, et des famines et des troubles: ces choses ne seront que les premières douleurs.
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
9 Mais prenez garde à vous-mêmes: car ils vous livreront aux Consistoires, et aux Synagogues; vous serez fouettés, et vous serez présentés devant les gouverneurs et devant les Rois, à cause de moi, pour leur être en témoignage.
“Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
10 Mais il faut que l'Evangile soit auparavant prêché dans toutes les nations.
Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
11 Et quand ils vous mèneront pour vous livrer, ne soyez point auparavant en peine de ce que vous aurez à dire, et n'y méditez point, mais tout ce qui vous sera donné [à dire] en ce moment-là, dites-le: car ce n'est pas vous qui parlez, mais le Saint-Esprit.
Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
12 Or le frère livrera son frère à la mort, et le père l'enfant, et les enfants se soulèveront contre leurs pères et leurs mères, et les feront mourir.
“Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
13 Et vous serez haïs de tous à cause de mon Nom; mais qui persévérera jusques à la fin, celui-là sera sauvé.
Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 Or quand vous verrez l'abomination qui cause la désolation qui a été prédite par Daniel le Prophète, être établie où elle ne doit point être (que celui qui lit [ce Prophète] y fasse attention!) alors que ceux qui seront en Judée s'enfuient aux montagnes.
“Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
15 Et que celui qui sera sur la maison, ne descende point dans la maison, et n'y entre point pour emporter quoi que ce soit de sa maison.
Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
16 Et que celui qui sera aux champs, ne retourne point en arrière pour emporter son habillement.
Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
17 Mais malheur à celles qui seront enceintes, et à celles qui allaiteront en ces jours-là.
Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
18 Or priez [Dieu] que votre fuite n'arrive point en hiver.
Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
19 Car en ces jours-là il y aura une telle affliction, qu'il n'y en a point eu de semblable depuis le commencement de la création des choses que Dieu a créées, jusqu'à maintenant, et il n'y en aura jamais qui l'égale.
Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
20 Et si le Seigneur n'eût abrégé ces jours-là, il n'y aurait personne de sauvé; mais il a abrégé ces jours, à cause des élus qu'il a élus.
“Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
21 Et alors si quelqu'un vous dit: voici, le Christ [est] ici; ou voici, [il est] là, ne le croyez point.
A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
22 Car il s'élèvera de faux christs et de faux prophètes, qui feront des prodiges et des miracles, pour séduire les élus mêmes, s'il était possible.
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
23 Mais donnez-vous-en garde; voici, je vous l'ai tout prédit.
Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
24 Or en ces jours-là, après cette affliction, le soleil sera obscurci, et la lune ne donnera point sa clarté;
“Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
25 Et les étoiles du ciel tomberont, et les vertus qui sont dans les cieux seront ébranlées.
taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
26 Et ils verront alors le Fils de l'homme venant sur les nuées, avec une grande puissance et une grande gloire.
“Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
27 Et alors il enverra ses Anges, et il assemblera ses élus, des quatre vents, depuis le bout de la terre jusques au bout au ciel.
Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
28 Or apprenez cette similitude prise du figuier: quand son rameau est en sève, et qu'il jette des feuilles, vous connaissez que l'été est proche.
“To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
29 Ainsi, quand vous verrez que ces choses arriveront, sachez qu'il est proche, et à la porte.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
30 En vérité je vous dis, que cette génération ne passera point, que toutes ces choses ne soient arrivées.
Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
31 Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
32 Or quant à ce jour et à cette heure, personne ne le sait, non pas même les Anges qui sont au ciel, ni même le Fils, mais [mon] Père [seul].
“Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
33 Faites attention [à tout], veillez et priez: car vous ne savez point quand ce temps arrivera.
Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
34 [C'est] comme si un homme allant dehors, et laissant sa maison, donnait de l'emploi à ses serviteurs, et à chacun sa tâche, et qu'il commandât au portier de veiller.
Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
35 Veillez donc: car vous ne savez point quand le Seigneur de la maison viendra, [si ce sera] le soir, ou à minuit, ou à l'heure que le coq chante, ou au matin;
“Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
36 De peur qu'arrivant tout à coup il ne vous trouve dormants.
In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
37 Or les choses que je vous dis, je les dis à tous; veillez.
Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”

< Marc 13 >