< Juges 21 >

1 Or ceux d'Israël avaient juré en Mitspa, en disant: Nul de nous ne donnera sa fille pour femme aux Benjamites.
Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
2 Puis le peuple vint à la maison du [Dieu] Fort, et ils demeurèrent là jusqu'au soir en la présence de Dieu; et ils élevèrent leurs voix, et pleurèrent amèrement,
Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
3 Et dirent: Ô Eternel, Dieu d'Israël! pourquoi ceci est-il arrivé en Israël, qu'une Tribu d'Israël ait été aujourd'hui retranchée?
Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
4 Et le lendemain le peuple se leva de bon matin, et bâtit là un autel, et ils offrirent des holocaustes, et des sacrifices de prospérités.
Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
5 Alors les enfants d'Israël dirent: Qui est celui d'entre toutes les Tribus d'Israël qui n'est point monté à l'assemblée vers l'Eternel? Car on avait fait un grand serment contre tout homme qui ne monterait point vers l'Eternel à Mitspa, en disant: Un tel sera puni de mort.
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
6 Car les enfants d'Israël se repentaient de ce qui était arrivé à Benjamin leur frère, et disaient aujourd'hui une Tribu a été retranchée d'Israël.
To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
7 Comment ferons-nous pour donner des femmes à ceux qui sont demeurés de reste, puisque nous avons juré par l'Eternel que nous ne leur donnerions point de nos filles pour femmes?
Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
8 Ils dirent donc: Y a-t-il quelqu'un d'entre les Tribus d'Israël qui ne soit point monté vers l'Eternel à Mitspa? Or voici, aucun homme de Jabès de Galaad n'était venu au camp, à l'assemblée.
Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
9 Car quand on fit le dénombrement du peuple, voici, il ne s'était trouvé aucun des habitants de Jabès de Galaad.
Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
10 C'est pourquoi l'assemblée y envoya douze mille hommes des plus vaillants, et leur commanda en disant: Allez, et frappez les habitants de Jabès de Galaad au tranchant de l'épée, tant les femmes que les petits enfants.
Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
11 Voici donc ce que vous ferez: Vous exterminerez à la façon de l'interdit tout mâle, et toute femme qui aura eu compagnie d'homme.
Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
12 Et ils trouvèrent entre les habitants de Jabès de Galaad quatre cents filles vierges, qui n'avaient point eu compagnie d'homme; et ils les amenèrent au camp à Silo, qui est au pays de Canaan.
Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
13 Alors toute l'assemblée envoya pour parler aux enfants de Benjamin qui étaient au rocher de Rimmon, et pour leur offrir la paix.
Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
14 En ce temps-là donc les Benjamites retournèrent, et on leur donna pour femmes celles qui avaient été conservées en vie d'entre les femmes de Jabès de Galaad; mais il ne s'en trouva pas [assez pour eux].
Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
15 Et le peuple se repentit de ce qui avait été fait à Benjamin; car l'Eternel avait fait une brèche aux Tribus d'Israël.
Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
16 Et les Anciens de l'assemblée dirent: Comment ferons-nous pour donner des femmes à ceux qui sont demeurés de reste; car les femmes ont été exterminées d'entre les Benjamites.
Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
17 Puis ils dirent: Ceux qui sont réchappés posséderont ce qui appartenait à Benjamin, afin qu'une Tribu d'Israël ne soit point effacée.
Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
18 Cependant nous ne leur pourrons point donner des femmes d'entre nos filles; car les enfants d'Israël ont juré, en disant: Maudit soit celui qui donnera une femme à ceux de Benjamin.
Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
19 Et ils dirent: Voici la solennité ordinaire de l'Eternel est à Silo, qui est vers l'Aquilon de Bethel, et au soleil levant du chemin qui monte de Bethel à Sichem, et au midi de Lebona.
Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
20 Et ils commandèrent aux enfants de Benjamin, en disant: Allez, et mettez des gens en embuscade aux vignes.
Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
21 Et quand vous verrez que les filles de Silo sortiront pour danser avec des flûtes, alors vous sortirez des vignes, et vous ravirez pour vous chacun sa femme d'entre les filles de Silo, et vous en irez au pays de Benjamin.
ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
22 Et quand leurs pères, ou leurs frères viendront vers nous pour plaider, nous leur dirons: Ayez pitié d'eux pour l'amour de nous, puisque nous n'avons point pris femme pour [chacun d'eux] en cette guerre, et vous serez coupables si vous ne leur en donnez point en un temps comme celui-ci.
Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
23 Les enfants de Benjamin firent ainsi, et enlevèrent des femmes selon leur nombre, d'entre celles qui dansaient, lesquelles ils ravirent; puis s'en allant ils retournèrent à leur héritage, et rebâtirent des villes, et y habitèrent.
Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
24 Ainsi en ce temps-là chacun des enfants d'Israël s'en alla de là en sa Tribu, et dans sa famille, et ils se retirèrent de là chacun dans son héritage.
A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
25 En ces jours-là il n'y avait point de Roi en Israël; mais chacun faisait ce qui lui semblait être droit.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.

< Juges 21 >