< Juges 20 >

1 Alors tous les enfants d'Israël sortirent, et tout le peuple fut assemblé comme si ce n'eût été qu'un seul homme, depuis Dan jusqu'à Beersebah, et jusqu'au pays de Galaad, vers l'Eternel, en Mitspa.
Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
2 Et les Cantons de tout le peuple, toutes les Tribus d'Israël, se trouvèrent à l'assemblée du peuple de Dieu, [au nombre de] quatre cent mille hommes de pied dégainant l'épée.
Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
3 (Or les enfants de Benjamin apprirent que les enfants d'Israël étaient montés en Mitspa.) Les enfants donc d'Israël dirent: Qu'on nous récite comment ce mal est arrivé.
(Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
4 Et le Lévite, mari de la femme tuée, répondit et dit: Etant arrivés à Guibha, qui est de Benjamin, moi et ma concubine, pour y passer la nuit;
Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
5 Les Seigneurs de Guibha se sont élevés contre moi, et ont environné de nuit la maison contre moi, prétendant me tuer; et ils ont tellement violé ma concubine qu'elle en est morte.
Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
6 C'est pourquoi ayant pris ma concubine, je l'ai mise en pièces, et je les ai envoyées par tous les quartiers de l'héritage d'Israël; car ils ont fait un crime énorme, et une action infâme en Israël.
Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
7 Vous voici tous, enfants d'Israël, délibérez-en ici entre vous, et donnez-en votre avis.
To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
8 Et tout le peuple se leva, comme si ce n'eût été qu'un seul homme, et ils dirent: Aucun de nous n'ira en sa tente, ni aucun de nous ne se retirera dans sa maison.
Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
9 Mais maintenant voici ce que nous ferons à Guibha, en procédant contr'elle par sort.
Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
10 Nous prendrons dix hommes de cent dans toutes les Tribus d'Israël, et cent de mille, et mille de dix mille, qui prendront de la provision pour le peuple, afin qu'étant entrés à Guibha de Benjamin, ils la traitent selon toute la turpitude qu'elle a commise en Israël.
Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
11 Ainsi tous ceux d'Israël furent assemblés contre cette ville-là, étant unis comme s'ils n'eussent été qu'un seul homme.
Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
12 Alors les Tribus d'Israël envoyèrent des hommes par toute la tribu de Benjamin pour lui dire: Quelle méchante action a-t-on [commise] parmi vous?
Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
13 Maintenant donc livrez-nous ces méchants hommes qui sont à Guibha, afin que nous les fassions mourir, et que nous ôtions le mal du milieu d'Israël. Mais les Benjamites ne voulurent point écouter la voix de leurs frères les enfants d'Israël.
Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
14 Mais les Benjamites sortant de leurs villes s'assemblèrent à Guibha, pour sortir en bataille contre les enfants d'Israël.
Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
15 Et en ce jour-là on fit le dénombrement des enfants de Benjamin qui étaient dans ces villes, [et il se trouva] vingt-six mille hommes, tirant l'épée, sans les habitants de Guibha, dont on fit aussi le dénombrement, qui furent sept cents hommes d'élite.
Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
16 De tout ce peuple-là il y avait sept cents hommes d'élite, desquels la main droite était serrée, tous tirant la pierre avec la fronde à un cheveu près, et ils n'y manquaient point.
Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
17 Et les hommes d'Israël furent [tous] dénombrés, excepté ceux de Benjamin, et il s'en trouva quatre cent mille hommes tirant l'épée, tous gens de guerre.
Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
18 Or ils partirent, et montèrent à la maison du [Dieu] Fort, et consultèrent Dieu. Les enfants donc d'Israël dirent: Qui est-ce d'entre nous qui montera le premier pour faire la guerre aux enfants de Benjamin? Et l'Eternel répondit: Juda [montera] le premier.
Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
19 Puis les enfants d'Israël se levèrent de bon matin, et campèrent près de Guibha.
Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
20 Et ceux d'Israël sortirent en bataille contre Benjamin, et rangèrent contr'eux [leur] armée près de Guibha.
Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
21 Et les enfants de Benjamin sortirent de Guibha, et en ce jour-là ils mirent par terre de ceux d'Israël vingt-deux mille hommes.
Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
22 Toutefois le peuple de ceux d'Israël reprit courage, et se rangea de nouveau en bataille au lieu où il s'était rangé le premier jour.
Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
23 Parce que les enfants d'Israël étaient montés, et avaient pleuré devant l'Eternel jusqu'au soir, et avaient consulté l'Eternel en disant: M'approcherai-je encore pour combattre contre les enfants de Benjamin, mon frère? Et l'Eternel avait répondu: Montez contre lui.
Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
24 Les enfants d'Israël s'approchèrent des enfants de Benjamin pour la seconde journée.
Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
25 Benjamin aussi sortit de Guibha contr'eux en cette seconde journée, et ils mirent encore par terre dix-huit mille hommes des enfants d'Israël, tous tirant l'épée.
A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
26 Alors tous les enfants d'Israël, et tout le peuple montèrent, et vinrent à la maison du [Dieu] Fort, et y pleurèrent, et se tinrent là devant l'Eternel, et jeûnèrent ce jour-là jusqu'au soir, et offrirent des holocaustes, et des sacrifices de prospérités devant l'Eternel.
Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
27 Ensuite les enfants d'Israël consultèrent l'Eternel, (or là était l'Arche de l'alliance de Dieu en ces jours-là.
Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
28 Et Phinées fils d'Eléazar, fils d'Aaron, se tenait devant l'Eternel en ces jours-là: ) [ils consultèrent donc l'Eternel] en disant: Sortirai-je encore une autre fois en bataille contre les enfants de Benjamin, mon frère, ou m'en désisterai-je? Et l'Eternel répondit: Montez, car demain je les livrerai entre vos mains.
Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
29 Et Israël mit une embuscade à l'entour de Guibha.
Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
30 Et les enfants d'Israël montèrent pour la troisième journée contre les enfants de Benjamin, et ils se rangèrent contre Guibha, comme les autres fois.
Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
31 Alors les enfants de Benjamin étant sortis à la rencontre du peuple, furent attirés hors de la ville, et commencèrent à frapper quelques-uns du peuple, environ trente hommes d'Israël qui furent blessés à mort comme les autres fois, dans les chemins, dont l'un monte à la maison du [Dieu] Fort; et l'autre à Guibha, parmi les champs.
Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
32 Et les enfants de Benjamin dirent: Ils tombent battus devant nous, comme la première fois. Mais les enfants d'Israël disaient: Fuyons, attirons-les hors de la ville, dans les chemins.
Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
33 Tous ceux d'Israël donc se levant de leur lieu, se rangèrent à Bahal-tamar; et les gens de l'embuscade aussi sortirent de leur lieu, [savoir de] la prairie de Guibha.
Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
34 Et dix mille hommes d'élite de tout Israël vinrent contre Guibha, et la mêlée fut rude; et ceux de [Benjamin] ne s'aperçurent point que le mal les atteignait.
Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
35 L'Eternel donc battit Benjamin devant les Israélites; et les enfants d'Israël mirent ce jour-là par terre vingt-cinq mille et cent hommes de Benjamin, tous tirant l'épée.
Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
36 Les enfants de Benjamin donc virent qu'ils étaient battus. Or ceux d'Israël avaient fait place à ceux de Benjamin; car ils s'assuraient sur l'embuscade qu'ils avaient mise près de Guibha.
Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
37 Et ceux qui étaient en embuscade se jetèrent incontinent sur Guibha; ainsi ceux qui étaient en embuscade marchèrent à la file, et frappèrent toute la ville au tranchant de l'épée.
Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
38 Or ceux d'Israël avaient donné pour signal à ceux qui étaient en embuscade, qu'ils fissent monter beaucoup de fumée de la ville.
Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
39 Ceux d'Israël donc avaient tourné le dos en la bataille, et Benjamin avait commencé de frapper et de blesser à mort environ trente hommes de ceux d'Israël; car ils disaient: Quoi qu'il en soit, certainement ils tombent battus devant nous, comme à la première bataille.
a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
40 Mais quand la fumée qui avait été élevée, commença à monter de la ville comme une colonne de fumée, Benjamin regarda derrière soi, et voici toute la ville montait en feu vers le ciel.
Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
41 Alors ceux d'Israël tournèrent visage et ceux de Benjamin furent épouvantés; car ils virent que le mal les avait atteints.
Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
42 Et ils tournèrent le dos devant ceux d'Israël vers le chemin du désert; mais l'armée [d'Israël] les serra de près. Et quant à ceux des villes, ils les mirent par terre, les ayant enfermés au milieu d'eux.
Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
43 Ils environnèrent [donc] ceux de Benjamin, [et] les poursuivirent, et les foulèrent aux pieds depuis Menuha jusqu'à l'opposite de Guibha, vers le soleil levant.
Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
44 Et il y eut de Benjamin dix-huit mille hommes tués, tous vaillants hommes.
Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
45 Alors [ceux de Benjamin] tournant le dos fuirent vers le désert au rocher de Rimmon, et [ceux d'Israël] en grappillèrent par les chemins cinq mille hommes, et les poursuivant de près jusqu'à Guidhom, ils en frappèrent deux mille hommes.
Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
46 Tous ceux donc qui tombèrent [morts] en ce jour-là de Benjamin, furent vingt-cinq mille hommes, tirant l'épée, [et] tous vaillants hommes.
A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
47 Et il y eut six cents hommes de ceux qui avaient tourné le dos, qui échappèrent vers le désert au rocher de Rimmon, et qui demeurèrent au rocher de Rimmon quatre mois.
Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
48 Et ceux d'Israël retournèrent vers les enfants de Benjamin, et les frappèrent au tranchant de l'épée, tant les hommes de chaque ville que les bêtes, et tout ce qui s'y trouva. Ils brûlèrent aussi toutes les villes qui s'y trouvèrent.
Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.

< Juges 20 >