< Josué 5 >
1 Or il arriva qu'aussitôt que tous les Rois des Amorrhéens qui [étaient] au deçà du Jourdain vers l'Occident, et tous les Rois des Cananéens qui étaient près de la mer, apprirent que l'Eternel avait fait tarir les eaux du Jourdain devant les enfants d'Israël, jusqu'à ce qu'ils fussent passés, leur cœur se fondit, et il n'y eut plus de courage en eux à cause des enfants d'Israël.
To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
2 En ce temps-là l'Eternel dit à Josué: Fais-toi des couteaux tranchants, et circoncis de nouveau pour une seconde fois les enfants d'Israël.
A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
3 Et Josué se fit des couteaux tranchants, et circoncit les enfants d'Israël au coteau des prépuces.
Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
4 Or la raison pour laquelle Josué les circoncit, c'est que tout le peuple qui était sorti d'Egypte, tous les mâles, [dis-je], hommes de guerre étaient morts au désert en chemin, après être sortis d'Egypte.
Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
5 Et que tout le peuple qui était sorti, avait bien été circoncis, mais ils n'avaient point circoncis aucun du peuple né dans le désert en chemin, après être sortis d'Egypte.
Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
6 Car les enfants d'Israël avaient marché par le désert quarante ans, jusqu'à ce qu'eut été consumé tout le peuple des gens de guerre qui étaient sortis d'Egypte, [et] qui n'avaient point obéi à la voix de l'Eternel; auxquels l'Eternel avait juré qu'il ne leur laisserait point voir le pays dont l'Eternel avait juré à leurs pères qu'il nous le donnerait, et qui est un pays découlant de lait et de miel.
Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
7 Et il avait suscité en leur place leurs enfants, lesquels Josué circoncit, parce qu'ils étaient incirconcis; car on ne les avait pas circoncis en chemin.
Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
8 Et quand on eut achevé de circoncire tout le peuple, ils demeurèrent en leur lieu au camp, jusqu'à ce qu'ils fussent guéris.
Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
9 Et l'Eternel dit à Josué: Aujourd'hui j'ai roulé de dessus vous l'opprobre d'Egypte. Et ce lieu-là a été nommé Guilgal jusqu'à aujourd'hui.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
10 Ainsi les enfants d'Israël se campèrent en Guilgal, et célébrèrent la Pâque le quatorzième jour du mois, sur le soir, dans les campagnes de Jérico.
Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
11 Et dès le lendemain de la Pâque, ils mangèrent du blé du pays, [savoir] des pains sans levain et du grain rôti, en ce même jour.
A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
12 Et la Manne cessa dès le lendemain, après qu'ils eurent mangé du blé du pays; et les enfants d'Israël n'eurent plus de Manne, mais ils mangèrent du crû de la terre de Canaan cette année-là.
Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
13 Or il arriva, comme Josué était près de Jérico, qu'il leva les yeux, et regarda; et voici, vis-à-vis de lui, se tenait debout un homme qui avait son épée nue en sa main; et Josué alla vers lui, et lui dit: Es-tu des nôtres, ou de nos ennemis?
To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
14 Et il dit: Non; mais je suis le chef de l'armée de l'Eternel, [qui] suis venu maintenant. Et Josué se jeta sur son visage en terre, et se prosterna, et lui dit: Qu'est-ce que mon Seigneur dit à son serviteur?
Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
15 Et le chef de l'armée de l'Eternel dit à Josué: Délie ton soulier de tes pieds; car le lieu sur lequel tu te tiens, est saint; et Josué [le] fit ainsi.
Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.