< Josué 3 >
1 Or Josué se leva de bon matin; ils partirent de Sittim, ils vinrent jusqu'au Jourdain, lui et tous les enfants d'Israël, et ils logèrent là cette nuit, avant qu'ils passassent.
Kashegari Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Shittim suka nufi Urdun inda suka sauka kafin su haye.
2 Et au bout de trois jours les officiers passèrent par le camp;
Bayan kwana uku sai shugabannin suka zazzaga sansani, suna
3 Et ils commandèrent au peuple en disant: Sitôt que vous verrez l'Arche de l'alliance de l'Eternel votre Dieu, et les Sacrificateurs de la race de Lévi qui la porteront, vous partirez de votre quartier, et vous marcherez après elle.
ba da umarni ga mutane, suna cewa, “Lokacin da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, da firistoci waɗanda su ne Lawiyawa, suna ɗauke da shi, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi.
4 Et afin que vous n'approchiez point d'elle, il y aura entre vous et elle une distance de la mesure d'environ deux mille coudées, afin que vous connaissiez le chemin par lequel vous devez marcher; car vous n'avez point ci-devant passé par ce chemin.
A ta haka za ku san inda za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai ku ɗan ba da rata wajen yadi ɗari tara tsakaninku da akwatin alkawari, kada ku kusace shi.”
5 Josué dit aussi au peuple: Sanctifiez-vous; car l'Eternel fera demain, au milieu de vous des choses merveilleuses.
Yoshuwa ya ce wa mutane, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai yi abubuwan al’ajabi a cikinku.”
6 Josué parla aussi aux Sacrificateurs, en disant: Chargez [sur vous] l'Arche de l'alliance, et passez devant le peuple. Ainsi ils chargèrent [sur eux] l'Arche de l'alliance, et marchèrent devant le peuple.
Yoshuwa ya ce wa firistoci, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku sha gaba.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban sauran jama’a.
7 Or l'Eternel avait dit à Josué: Aujourd'hui je commencerai de t'élever à la vue de tout Israël; afin qu'ils connaissent que comme j'ai été avec Moïse, je serai [aussi] avec toi.
Ubangiji kuwa ya ce wa Yoshuwa, “Yau, zan fara ɗaukaka ka a gaban Isra’ilawa duka don su sani cewa ina tare da kai kamar yadda na kasance tare da Musa.
8 Tu commanderas donc aux Sacrificateurs qui portent l'Arche de l'alliance, en [leur] disant: Sitôt que vous arriverez au bord de l'eau du Jourdain, vous vous arrêterez au Jourdain.
Ka ce wa firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, ‘Sa’ad da kuka kai bakin Urdun, ku shiga cikin ruwan ku tsaya.’”
9 Et Josué dit aux enfants d'Israël: Approchez-vous d'ici, et écoutez les paroles de l'Eternel votre Dieu.
Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Ku zo nan ku ji maganar Ubangiji Allahnku.
10 Puis Josué dit: Vous reconnaîtrez à ceci que le [Dieu] Fort, [et] vivant, est au milieu de vous, et qu'il chassera certainement de devant vous les Cananéens, les Héthiens, les Héviens, les Phérésiens, les Guirgasiens, les Amorrhéens, et les Jébusiens.
Ta haka ne za ku san cewa Allah mai rai yana tare da ku, kuma ba shakka a gabanku za ku gani zai kore Kan’aniyawa, Hittiyawa, Hiwiyawa, Ferizziyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa da Yebusiyawa.
11 Voici, l'Arche de l'alliance du Dominateur de toute la terre s'en va passer devant vous au travers du Jourdain.
Ku duba, akwatin alkawarin Ubangiji na dukan duniya zai yi gaba cikin Urdun kafin ku.
12 Maintenant donc choisissez douze hommes des Tribus d'Israël, un homme de chaque Tribu.
Yanzu sai ku zaɓi mutum goma sha biyu daga kabilan Isra’ila, ɗaya daga kowace kabila.
13 Et il arrivera qu'aussitôt que les plantes des pieds des Sacrificateurs qui portent l'Arche de l'Eternel, le Dominateur de toute la terre, seront posées dans les eaux du Jourdain, les eaux du Jourdain seront coupées, les eaux, [dis-je], qui descendent d'en haut, et elles s'arrêteront en un monceau.
Kuma da firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangiji dukan duniya, sun sa ƙafa cikin ruwan kogin Urdun, ruwan da yake gudu a rafin zai tsaya cik yă taru a wuri ɗaya.”
14 Et il arriva que le peuple étant parti de ses tentes pour passer le Jourdain, les Sacrificateurs qui portaient l'Arche de l'alliance, étaient devant le peuple.
Saboda haka sa’ad da mutanen suka tashi don su ƙetare Urdun, firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin suka sha gaba.
15 Et sitôt que ceux qui portaient l'Arche furent arrivés au Jourdain, et que les pieds des Sacrificateurs qui portaient l'Arche furent mouillés au bord de l'eau, (or le Jourdain regorge par dessus tous ses bords durant tout le temps de la moisson.)
Da kaka Urdun yakan cika makil da ruwa. Duk da haka da zarar firistoci masu ɗauke da akwatin alkawari suka tsoma ƙafafunsu a gefen ruwa,
16 Les eaux qui descendaient d'en-haut, s'arrêtèrent, et s'élevèrent en un monceau fort loin, depuis la ville d'Adam, qui [est] à côté de Tsartan; et celles [d'embas], qui descendaient vers la mer de la campagne, qui est la mer salée, défaillirent et s'écoulèrent, et le peuple passa vis-à-vis de Jérico.
sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru a wuri ɗaya ya yi tudu daga nan har zuwa wani garin da ake kira Adam kusa da Zaretan, ruwan da yake gangarowa zuwa Tekun Araba (Tekun Gishiri) kuma ya yanke gaba ɗaya. Sai mutane suka ƙetare kusa da Yeriko.
17 Mais les Sacrificateurs qui portaient l'Arche de l'alliance de l'Eternel, s'arrêtèrent [de pied] ferme sur le sec au milieu du Jourdain, pendant que tout Israël passa à sec, jusqu'à ce que tout le peuple eût achevé de passer le Jourdain.
Firistocin kuwa da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya daram a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Urdun a lokacin da Isra’ilawa suka ƙetarewa, har sai da dukan mutane suka gama ƙetarewa.