< Josué 19 >
1 Le deuxième sort échut à Siméon, pour la Tribu des enfants de Siméon selon leurs familles, et leur héritage fut parmi l'héritage des enfants de Juda.
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 Et ils eurent dans leur héritage Béer-sebah, Sebah, Molada,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 Hatsar-suhal, Bala, Hetsem,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 Eltolad, Bethul, Horma,
Eltolad, Betul, Horma,
5 Tsiklag, Beth-marcaboth, Hatsar-susa,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 Beth-lebaoth et Saruhen; treize villes et leurs villages.
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 Hajin, Rimmon, Hether, et Hasan; quatre villes et leurs villages.
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 Et tous les villages qui étaient autour de ces villes-là jusqu'à Balath-béer, qui est Rama du Midi. Tel fut l'héritage de la Tribu des enfants de Siméon, selon leurs familles.
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 L'héritage des enfants de Siméon fut pris du lot des enfants de Juda; car la part des enfants de Juda était trop grande pour eux; c'est pourquoi les enfants de Siméon eurent leur héritage parmi le leur.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 Le troisième sort monta pour les enfants de Zabulon, selon leurs familles; et la frontière de leur héritage fut jusqu'à Sarid.
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 Et leur frontière devait monter vers le quartier devers la mer, même jusqu'à Marhala, puis se rencontrer à Dabbeseth, et de là au torrent qui est vis-à-vis de Jokneham.
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 Or [cette frontière] devait retourner de Sarid vers l'Orient, au soleil levant vers les confins de Kislothtabor, puis sortir vers Dabrath, et monter à Japhiah;
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 Puis de là passer vers l'Orient, au Levant, à Guitta-hépher qui est Hittakatsin, puis sortir, à Rimmon-Methoar, qui est Neha.
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 Puis cette frontière devait tourner du côté du Septentrion à Hannathon; et ses extrémités devaient se rendre en la vallée de Jiphtahel.
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 Avec Kattath, Nahalal, Simron, Jidéala, et Beth-lehem; il y avait douze villes, et leurs villages.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 Tel fut l'héritage des enfants de Zabulon selon leurs familles; ces villes-là, et leurs villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 Le quatrième sort échut à Issacar, pour les enfants d'Issacar, selon leurs familles.
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 Et leur contrée fut ce qui est vers Jizrehel, Kesulloth, Sunem,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 Hapharjim, Sion, Anaharath,
Hafarayim, Anaharat,
20 Rabbith, Kisjon, Ebets,
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 Remeth, Hen-gannim, Hen-hadda et Beth-patsets.
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 Et la frontière se devait rencontrer à Tabor et vers Sabatsim, et à Beth-semes; tellement que les extrémités de leur frontière se devaient rendre au Jourdain; seize villes, et leurs villages.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 Tel fut l'héritage de la Tribu des enfants d'Issacar, selon leurs familles, ces villes-là, et leurs villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 Le cinquième sort échut à la Tribu des enfants d'Aser, selon leurs familles.
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 Et leur frontière fut Helkath, Hali, Beten, Acsaph,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 Alammélec, Hamhad et Miséal; et elle se devait rencontrer à Carmel, [au quartier] vers la mer, et à Sihor vers Benath.
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 Puis elle devait retourner vers le soleil levant, à Beth-dagon, et se rencontrer en Zabulon, et à la vallée de Jiphtahel vers le Septentrion, [et à] Beth-hemek et Nehiel; puis sortir à main gauche vers Cabul.
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 Et Hébron, et Rehob, et Hammon, et Cana, jusqu'à Sidon la grande.
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 Puis la frontière devait retourner à Rama, même jusqu'à Tsor, ville forte; puis cette frontière devait retourner à Hosa; tellement que ses extrémités, se devaient rendre au quartier qui est vers la mer, depuis la portion tirant vers Aczib;
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 Avec Hummah, et Aphek, et Rehob; vingt-deux villes, et leurs villages.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 Tel fut l'héritage de la Tribu des enfants d'Aser, selon leurs familles; ces villes-là et leurs villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 Le sixième sort échut aux enfants de Nephthali, pour les enfants de Nephthali, selon leurs familles.
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 Et leur frontière fut depuis Heleph, [et] depuis Allon à Tsahannim, et Adami-nekeb, et Jabnéel jusqu'à Lakkum, tellement que ses extrémités se devaient rendre au Jourdain.
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 Puis cette frontière devait retourner du côté d'Occident, vers Aznoth-Tabor, et sortir de là à Hukkok; tellement que du côté du Midi elle devait se rencontrer en Zabulon, et du côté d'Occident elle devait se rencontrer en Aser. Or jusqu'en Juda le Jourdain [était au] soleil levant.
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 Au reste, les villes closes étaient Tsiddim, Tser, Hammath, Rakkath, Kinnereth,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
37 Kédès, Edréhi, Hen-Hatsor,
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 Jireon, Migdal-el, Harem, Beth-hanath et Beth-semes; dix-neuf villes et leurs villages.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 Tel fut l'héritage de la Tribu des enfants de Nephthali, selon leurs familles; ces villes-là, et leurs villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 Le septième sort échut à la Tribu des enfants de Dan selon leurs familles.
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 Et la contrée de leur héritage fut, Tsorah, Estaol, Hir-semes,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 Sahalabim, Ajalon, Jithla,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 Elon, Timnatha, Hekron,
Elon, Timna, Ekron,
44 Elteké, Guibbethon, Bahalath,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 Jehud, Bené-berak, Gath-rimmon,
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 Me-jarkon, et Rakkon, avec les limites qui sont vis-à-vis de Japho.
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 Or la contrée qui était échue aux enfants de Dan, était [trop petite] pour eux; c'est pourquoi les enfants de Dan montèrent, et combattirent contre Lesem, et la prirent, et la frappèrent au tranchant de l'épée, et la possédèrent, et y habitèrent; et ils appelèrent Lesem, Dan, du nom de Dan leur père.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 Tel fut l'héritage de la Tribu des enfants de Dan selon leurs familles; ces villes-là, et leurs villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 Au reste après qu'on eut achevé de partager le pays selon ses confins, les enfants d'Israël donnèrent un héritage parmi eux à Josué fils de Nun.
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 Selon le commandement de l'Eternel; ils lui donnèrent la ville qu'il demanda; [savoir] Timnath-sérah en la montagne d'Ephraïm; et il bâtit la ville, et y habita.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 Ce sont là les héritages qu'Eléazar le Sacrificateur, et Josué, fils de Nun, et les chefs des pères des Tribus des enfants d'Israël partagèrent par sort en Silo, devant l'Eternel, à l'entrée du Tabernacle d'assignation, et ils achevèrent [ainsi] de partager le pays.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.