< Joël 1 >
1 La parole de l'Eternel qui fut [adressée] à Joël, fils de Péthuel.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Anciens, écoutez ceci, et vous, tous les habitants du pays, prêtez l'oreille. Est-il arrivé de votre temps, ou même du temps de vos pères, une chose comme celle-ci?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Faites-en le récit à vos enfants, et que vos enfants le fassent à leurs enfants, et leurs enfants à une autre génération.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 La sauterelle a brouté les restes du hanneton, et le hurebec a brouté les restes de la sauterelle, et le vermisseau a brouté les restes du hurebec.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Ivrognes, réveillez-vous, et pleurez; et vous tous buveurs de vin hurlez à cause du vin nouveau, parce qu'il est retranché à votre bouche.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 Car une nation puissante et innombrable est montée contre mon pays; ses dents sont des dents de lion, et elle a les dents mâchelières d'un vieux lion.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 Elle a réduit ma vigne en désert, et a ôté l'écorce de mes figuiers; elle les a entièrement dépouillés, et les a abattus, leurs branches en sont devenues blanches.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Lamente-toi comme une jeune femme qui se serait ceinte d'un sac, à cause [de la mort] du mari de sa jeunesse.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 Le gâteau et l'aspersion sont retranchés de la maison de l'Eternel, et les Sacrificateurs qui font le service de l'Eternel mènent deuil.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 Les champs sont ravagés, la terre mène deuil parce que le froment est ravagé, que le vin doux est tari, et que l'huile manque.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 Laboureurs soyez confus; vignerons hurlez à cause du froment et de l'orge; car la moisson des champs est périe.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 Les vignes sont sans fruit, et les figuiers ont manqué; les grenadiers, et les palmiers, les pommiers et tous les arbres des champs ont séché, c'est pourquoi la joie a cessé entre les hommes.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Sacrificateurs ceignez-vous, et lamentez; vous qui faites le service de l'autel, hurlez, vous qui faites le service de mon Dieu entrez, passez la nuit vêtus de sacs, car il est défendu au gâteau et à l'aspersion d'entrer en la maison de votre Dieu.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Sanctifiez le jeûne, publiez l'assemblée solennelle, assemblez les anciens, et tous les habitants du pays en la maison de l'Eternel votre Dieu, et criez à l'Eternel; [en disant]:
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 Hélas, quelle journée! car la journée de l'Eternel est proche, et elle viendra comme un dégât fait par le Tout-puissant.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Les vivres ne sont-ils pas retranchés de devant nos yeux; et la joie et l'allégresse, de la maison de notre Dieu?
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 Les grains sont pourris sous leurs mottes, les greniers sont désolés, c'en est fait des granges, parce que le froment a manqué.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Ô combien ont gémi les bêtes, et dans quelle peine ont été les troupeaux de bœufs, parce qu'ils n'ont point de pâturage! Aussi les troupeaux de brebis sont désolés.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 Eternel, je crierai à toi, car le feu a consumé les cabanes du désert, et la flamme a brûlé tous les arbres des champs.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 Même toutes les bêtes des champs crient à toi, parce que les cours des eaux sont taris, et que le feu a consumé les cabanes du désert.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.