< Job 6 >

1 Mais Job répondit, et dit:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Plût à Dieu que mon indignation fût bien pesée, et qu'on mît ensemble dans une balance ma calamité!
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 Car elle serait plus pesante que le sable de la mer; c'est pourquoi mes paroles sont englouties.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 Parce que les flèches du Tout-puissant sont au dedans de moi; mon esprit en suce le venin; les frayeurs de Dieu se dressent en bataille contre moi.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 L'âne sauvage braira-t-il après l'herbe, et le bœuf mugira-t-il après son fourrage?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Mangera-t-on sans sel ce qui est fade? trouvera-t-on de la saveur dans le blanc d'un œuf?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 Mais pour moi, les choses que je n'aurais pas seulement voulu toucher, sont des saletés qu'il faut que je mange.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 Plût à Dieu que ce que je demande m'arrivât, et que Dieu me donnât ce que j'attends;
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 Et que Dieu voulût m'écraser, et [qu'il voulût] lâcher sa main pour m'achever!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 Mais j'ai encore cette consolation, quoique la douleur me consume, et qu'elle ne m'épargne point, que je n'ai point tû les paroles du Saint.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 Quelle est ma force, que je puisse soutenir [de si grands maux]? et quelle [en est] la fin, que je puisse prolonger ma vie?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Ma force est-elle une force de pierre, et ma chair est-elle d'acier?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Ne suis-je pas destitué de secours, et tout appui n'est-il pas éloigné de moi?
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 A celui qui se fond [sous l'ardeur des maux, est due] la compassion de son ami; mais il a abandonné la crainte du Tout-puissant.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 Mes frères m'ont manqué comme un torrent, comme le cours impétueux des torrents qui passent;
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Lesquels on ne voit point à cause de la glace, et sur lesquels s'entasse la neige;
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 Lesquels, au temps que la chaleur donne dessus, défaillent; quand ils sentent la chaleur, ils disparaissent de leur lieu;
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 Lesquels serpentant çà et là par les chemins, se réduisent à rien, et se perdent.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Les troupes des voyageurs de Téma y pensaient, ceux qui vont en Séba s'y attendaient;
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 [Mais] ils sont honteux d'y avoir espéré; ils y sont allés, et ils en ont rougi.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Certes, vous m'êtes devenus inutiles; vous avez vu ma calamité étonnante, et vous en avez eu horreur.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Est-ce que je vous ai dit: Apportez-moi et me faites des présents de votre bien?
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Et délivrez-moi de la main de l'ennemi, et me rachetez de la main des terribles?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Enseignez-moi, et je me tairai; et faites-moi entendre en quoi j'ai erré.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 Ô combien sont fortes les paroles de vérité! mais votre censure, à quoi tend-elle?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Pensez-vous qu'il ne faille avoir que des paroles pour censurer; et que les discours de celui qui est hors d'espérance, ne soient que du vent?
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 Vous vous jetez même sur un orphelin, et vous percez votre intime ami.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Mais maintenant je vous prie regardez-moi bien, si je mens en votre présence!
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Revenez, je vous prie, [et] qu'il n'y ait point d'injustice [en vous]; oui, revenez encore; car je ne suis point coupable en cela.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Y a-t-il de l'iniquité en ma langue? et mon palais ne sait-il pas discerner mes calamités?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?

< Job 6 >