< Job 42 >

1 Alors Job répondit à l'Eternel, et dit:
Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
2 Je sais que tu peux tout, et qu'on ne te saurait empêcher de faire ce que tu penses.
“Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
3 Qui est celui-ci, [as-tu dit], qui étant sans science, [entreprend] d'obscurcir [mon] conseil? J'ai donc parlé, et je n'y entendais rien; ces choses sont trop merveilleuses pour moi, et je n'[y] connais rien.
Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
4 Ecoute maintenant, et je parlerai; je t'interrogerai, et tu m'enseigneras.
“Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
5 J'avais ouï de mes oreilles parler de toi; mais maintenant mon œil t'a vu.
Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
6 C'est pourquoi j'ai horreur [d'avoir ainsi parlé], et je m'en repens sur la poudre et sur la cendre.
Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
7 Or après que l'Eternel eut dit ces paroles à Job, il dit à Eliphas Témanite: Ma fureur est embrasée contre toi, et contre tes deux compagnons; parce que vous n'avez pas parlé droitement de moi comme Job mon serviteur.
Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
8 C'est pourquoi prenez maintenant sept taureaux, et sept béliers, et allez vers Job mon serviteur, et offrez un holocauste pour vous, et Job mon serviteur priera pour vous; (car certainement j'exaucerai sa prière, ) afin que je ne vous traite pas selon votre folie; parce que vous n'avez pas parlé droitement devant moi, comme a fait Job mon serviteur.
Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
9 Ainsi Eliphas Témanite, et Bildad Suhite, [et] Tsophar Nahamathite vinrent, et firent ce que l'Eternel leur avait commandé; et l'Eternel exauça la prière de Job.
Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
10 Et l'Eternel tira Job de sa captivité quand il eut prié pour ses amis; et il rendit à Job le double de tout ce qu'il avait eu.
Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
11 Aussi tous ses frères, et toutes ses sœurs, et tous ceux qui l'avaient connu auparavant, vinrent vers lui, et mangèrent avec lui dans sa maison, et lui ayant témoigné qu'ils compatissaient à son état, ils le consolèrent de tout le mal, que l'Eternel avait fait venir sur lui; et chacun d'eux lui donna une pièce d'argent, et chacun une bague d'or.
Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
12 Ainsi l'Eternel bénit le dernier état de Job plus que le premier, tellement qu'il eut quatorze mille brebis, et six mille chameaux, et mille couples de bœufs, et mille ânesses.
Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
13 Il eut aussi sept fils, et trois filles.
Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
14 Et il appela le nom de l'une Jémina, et le nom de l'autre Ketsiha, et le nom de la troisième Kéren-happuch.
’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
15 Et il ne se trouva point dans tout le pays de si belles femmes, que les filles de Job; et leur père leur donna héritage entre leurs frères.
Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
16 Et Job vécut après ces choses-là cent quarante ans, et il vit ses fils, et les fils de ses fils, jusqu'à la quatrième génération.
Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
17 Puis il mourut âgé et rassasié de jours.
Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.

< Job 42 >