< Job 40 >

1 L'Eternel prit encore la parole, et dit:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 Celui qui conteste avec le Tout-puissant, lui apprendra-t-il quelque chose? Que celui qui dispute avec Dieu, réponde à ceci.
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 Alors Job répondit à l'Eternel, et dit:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 Voici, je suis un homme vil; que te répondrais-je? Je mettrai ma main sur ma bouche.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 J'ai parlé une fois, mais je ne répondrai plus; j'ai même parlé deux fois, mais je n'y retournerai plus.
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 Et l'Eternel parla encore à Job du milieu d'un tourbillon, et lui dit:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Ceins maintenant tes reins comme un vaillant homme; je t'interrogerai, et tu m'enseigneras.
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Anéantiras-tu mon jugement? me condamneras-tu pour te justifier?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 Et as-tu un bras comme le [Dieu] Fort? tonnes-tu de la voix comme lui?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Pare-toi maintenant de magnificence et de grandeur, et revêts-toi de majesté et de gloire.
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Répands les ardeurs de ta colère, regarde tout orgueilleux, et l'abats.
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 Regarde tout orgueilleux, abaisse-le, et froisse les méchants sur la place.
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Cache-les tous ensemble dans la poudre, et bande leur visage dans un lieu caché.
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 Alors je te donnerai moi-même cette louange, que ta droite t'aura sauvé.
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Or voilà le Béhémoth que j'ai fait avec toi; il mange le foin comme le bœuf.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Voilà maintenant, sa force est en ses flancs, et sa vertu est dans le nombril de son ventre.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 Il remue sa queue, qui est comme un cèdre; les nerfs de ses épouvantements sont entrelacés.
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 Ses os sont des barres d'airain, [et] ses menus os sont comme des barreaux de fer.
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 C'est le chef-d'œuvre du [Dieu] Fort; celui qui l'a fait lui a donné son épée.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 Et les montagnes lui rapportent leur revenu, et c'est là que se jouent toutes les bêtes des champs.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Il se couche dans les lieux où il y a de l'ombre, au milieu des roseaux et des marécages.
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Les arbres touffus le couvrent de leur ombre, et les saules des torrents l'environnent.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Voilà, il engloutit une rivière [en buvant], et il ne s'en retire pas vite; et il ne s'étonnerait pas quand le Jourdain se dégorgerait dans sa gueule.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 Il l'engloutit en le voyant, et son nez passe au travers des empêchements qu'il rencontre.
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?

< Job 40 >