< Job 4 >

1 Alors Eliphas Témanite prit la parole, et dit:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Si nous entreprenons de te parler, te fâcheras-tu? mais qui pourrait s'empêcher de parler?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Voilà, tu en as enseigné plusieurs, et tu as renforcé les mains lâches.
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Tes paroles ont affermi ceux qui chancelaient, et tu as fortifié les genoux qui pliaient.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 Et maintenant que ceci t'est arrivé, tu t'en fâches! il t'a atteint, et tu en es tout troublé.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Ta piété n'a-t-elle pas été ton espérance? et l'intégrité de tes voies [n'a-t-elle pas été] ton attente?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Rappelle, je te prie, dans ton souvenir, où est l'innocent qui ait jamais péri, et où les hommes droits ont-ils [jamais] été exterminés?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 Mais j'ai vu que ceux qui labourent l'iniquité, et qui sèment l'outrage, les moissonnent.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 Ils périssent par le souffle de Dieu, et ils sont consumés par le vent de ses narines.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 [Il étouffe] le rugissement du lion, et le cri d'un grand lion, et il arrache les dents des lionceaux.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 Le lion périt par faute de proie, et les petits du vieux lion sont dissipés.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Mais quant à moi, une parole m'a été adressée en secret, et mon oreille en a entendu quelque peu.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 Pendant les pensées diverses des visions de la nuit, quand un profond sommeil saisit les hommes,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 Une frayeur et un tremblement me saisirent qui étonnèrent tous mes os.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Un esprit passa devant moi, [et] mes cheveux en furent tout hérissés.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 Il se tint là, mais je ne connus point son visage; une représentation était devant mes yeux, et j'ouïs une voix basse [qui disait]:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 L'homme sera-t-il plus juste que Dieu? l'homme sera-t-il plus pur que celui qui l'a fait?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Voici, il ne s'assure point sur ses serviteurs, et il met la lumière dans ses Anges:
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 Combien moins [s'assurera-t-il] en ceux qui demeurent dans des maisons d'argile; en ceux dont le fondement est dans la poussière, et qui sont consumés à la rencontre d'un vermisseau?
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 Du matin au soir ils sont brisés, et, sans qu'on s'en aperçoive, ils périssent pour toujours.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 L'excellence qui était en eux, n'a-t-elle pas été emportée? Ils meurent sans être sages.
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

< Job 4 >