< Job 38 >

1 Alors l'Eternel répondit à Job du milieu d'un tourbillon, et lui dit:
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Qui est celui-ci qui obscurcit le conseil par des paroles sans science?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Ceins maintenant tes reins comme un vaillant homme, et je t'interrogerai, et tu me feras voir quelle est ta science.
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Où étais-tu quand je fondais la terre? dis-le-moi, si tu as de l'intelligence.
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Qui est-ce qui en a réglé les mesures? le sais-tu? ou qui est-ce qui a appliqué le niveau sur elle?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Sur quoi sont plantés ses pilotis, ou qui est celui qui a posé la pierre angulaire pour la soutenir.
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 Quand les étoiles du matin se réjouissaient ensemble, et que les fils de Dieu chantaient en triomphe?
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 Qui est-ce qui a renfermé la mer dans ses bords, quand elle fut tirée de la matrice, [et] qu'elle en sortit?
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 Quand je mis la nuée pour sa couverture, et l'obscurité pour ses langes?
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 Et que j'établis sur elle mon ordonnance, et lui mis des barrières et des portes?
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 Et lui dis: Tu viendras jusque là, et tu ne passeras point plus avant, et ici s'arrêtera l'élévation de tes ondes.
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 As-tu, depuis que tu es au monde, commandé au point du jour; et as-tu montré à l'aube du jour le lieu où elle doit se lever?
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 Afin qu'elle saisisse les extrémités de la terre, et que les méchants se retirent à l'écart,
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 Et qu'elle prenne une nouvelle forme, comme une argile figurée; et que [toutes choses y] paraissent comme avec de [nouveaux] habits,
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 Et que la clarté soit défendue aux méchants, et que le bras élevé soit rompu?
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Es-tu venu jusqu'aux gouffres de la mer, et t'es-tu promené au fond des abîmes?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Les portes de la mort se sont-elles découvertes à toi? as-tu vu les portes de l'ombre de la mort?
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 As-tu compris toute l'étendue de la terre? si tu l'as toute connue, montre-le.
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 En quel endroit se tient la lumière, et où est le lieu des ténèbres?
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 Que tu ailles prendre l'une et l'autre en son quartier, et que tu saches le chemin de leur maison?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Tu le sais; car alors tu naquis, et le nombre de tes jours est grand.
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Es-tu entré dans les trésors de la neige? As-tu vu les trésors de la grêle,
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 Laquelle je retiens pour le temps de l'affliction, et pour le jour du choc et du combat?
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Par quel chemin se partage la lumière, [et par quelle voie] le vent d'Orient se répand-il sur la terre?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Qui est-ce qui a ouvert les conduits aux inondations, et le chemin à l'éclair des tonnerres,
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 Pour faire pleuvoir sur une terre où il n'y a personne, et sur le désert où il ne demeure aucun homme.
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 Pour arroser abondamment les lieux solitaires et déserts, et pour faire pousser le germe de l'herbe?
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 La pluie n'a-t-elle point de père? ou qui est-ce qui produit les gouttes de la rosée?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 Du ventre de qui sort la glace? et qui est-ce qui engendre le frimas du ciel?
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 Les eaux se cachent étant durcies comme une pierre, et le dessus de l'abîme se prend.
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Pourrais-tu retenir les délices de la Poussinière, ou faire lever les tempêtes [qu'excite] la constellation d'Orion?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Peux-tu faire lever en leur temps les signes du Zodiaque? et conduire la petite Ourse avec les étoiles?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Connais-tu l'ordre des cieux, et disposeras-tu de leur gouvernement sur la terre?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Crieras-tu à haute voix à la nuée, afin qu'une abondance d'eaux t'arrose?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Enverras-tu les foudres de sorte qu'elles partent, et te disent: Nous voici?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Qui est-ce qui a mis la sagesse dans les reins? ou qui a donné au cœur l'intelligence?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Qui est-ce qui a assez d'intelligence pour compter les nuées, et pour placer les outres des cieux,
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 Quand la poudre est détrempée par les eaux qui l'arrosent, et que les fentes [de la terre] viennent à se rejoindre?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Chasseras-tu de la proie pour le vieux lion, et rassasieras-tu les lionceaux qui cherchent leur vie,
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 Quand ils se tapissent dans leurs antres, et qu'ils se tiennent dans leurs forts aux aguets?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Qui est-ce qui apprête la nourriture au corbeau, quand ses petits crient au [Dieu] Fort, et qu'ils vont errants, parce qu'ils n'ont point de quoi manger?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?

< Job 38 >