< Job 37 >

1 Mon cœur même à cause de cela est en émotion, et sort [comme] de sa place.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Ecoutez attentivement et en tremblant le bruit qu'il fait, et le son éclatant qui sort de sa bouche.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Il le fait aller sous tous les cieux, et son feu étincelant jusqu'aux extrémités de la terre.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Après lui s'élève un grand bruit; il tonne de sa voix magnifique, et il ne tarde point après que sa voix a été ouïe.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Le [Dieu] Fort tonne prodigieusement par sa voix, [et] il fait des choses grandes, que nous ne saurions comprendre.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Car il dit à la neige: Sois sur la terre; et [il le dit aussi] à l'ondée de la pluie, à l'ondée, dis-je, des pluies de sa force.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Alors il fait que chacun se renferme chez soi pour reconnaître tous les gens qu'il a à son ouvrage.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Les bêtes se retirent dans les tanières, et se tiennent dans leurs repaires.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Le vent orageux vient du fond du Midi; et le froid vient des vents du Septentrion.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Le [Dieu] Fort par son souffle donne la glace, et les eaux qui se répandaient au large, sont mises à l'étroit.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Il lasse aussi la nuée à force d'arroser; et il écarte les nuées par sa lumière.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 Et elles font plusieurs tours selon ses desseins pour faire tout ce qu'il leur a commandé, sur la face de la terre habitable.
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 Il les fait venir, soit pour s'en servir de verge, soit pour la terre, soit pour répandre ses bienfaits.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Fais attention à ceci, Job; arrête-toi; considère les merveilles du [Dieu] Fort.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Sais-tu comment Dieu les arrange, et comment il fait briller la lumière de sa nuée?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Connais-tu le balancement des nuées, et les merveilles de celui qui est parfait en science?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Pourquoi tes vêtements sont chauds, quand il donne du relâche à la terre par le vent du Midi?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 As-tu étendu avec lui les cieux, qui sont fermes comme un miroir de fonte?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Montre-nous ce que nous lui dirons; car nous ne saurions rien dire par ordre à cause de nos ténèbres.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Lui racontera-t-on quand j'aurai parlé? S'il y a un homme qui en parle, certainement il en sera englouti.
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Et maintenant, on ne voit point la lumière, quand elle resplendit dans les cieux; après que le vent y a passé, et qu'il les a nettoyés.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 [Et que le temps qui reluit comme] l'or, est venu du Septentrion. Il y a en Dieu une majesté redoutable.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 C'est le Tout-puissant; on ne le saurait comprendre; il est grand en puissance, en jugement, et en abondance de justice; il n'opprime personne.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 C'est pourquoi les hommes le craignent; mais il ne les voit pas tous sages de cœur.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Job 37 >