< Job 35 >
1 Elihu poursuivit encore son discours, et dit:
Sai Elihu ya ce,
2 As-tu pensé rendre ta cause bonne, [quand] tu as dit: Ma justice [est] au-dessus de celle du [Dieu] Fort?
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 Si tu demandes de quoi elle te profitera, [disant]: Que m'en reviendra-t-il, de même que de mon péché?
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 Je te répondrai en ces termes, et à tes amis qui sont avec toi.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Regarde les cieux, et les contemple; vois les nuées, elles sont plus hautes que toi.
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 Si tu pèches, quel mal fais-tu à Dieu? et quand tes péchés se multiplieront, quel mal en recevra-t-il?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 Si tu es juste, que lui donnes-tu? et qu'est-ce qu'il reçoit de ta main?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 C'est à un homme, comme tu es, que ta méchanceté [peut nuire]; et c'est au fils d'un homme que ta justice [peut être utile].
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 On fait crier les opprimés par la grandeur [des maux qu'on leur fait]; ils crient à cause de la violence des grands.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 Et on ne dit point: où est le Dieu qui m'a fait, [et] qui donne de quoi chanter pendant la nuit;
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 Qui nous rend plus éclairés que les animaux de la terre, et plus intelligents que les oiseaux des cieux?
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 On crie donc à cause de la fierté des méchants; mais Dieu ne les exauce point.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Cependant [tu ne dois pas dire] que ce soit en vain; que le [Dieu] Fort n'écoute point, et que le Tout-puissant n'y a nul égard.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Encore moins lui dois-tu dire; tu ne le vois point; car le jugement est devant lui; attends-le donc.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 Mais maintenant, ce n'est rien ce que sa colère exécute, et il n'est point entré fort avant en connaissance de toutes les choses que tu as faites.
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Job donc a ouvert sans raison sa bouche [pour se plaindre], et il a entassé paroles sur paroles, sans connaissance.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”