< Job 27 >

1 Et Job continuant reprit son discours sentencieux, et dit:
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 Le [Dieu] Fort, qui a mis mon droit à l'écart, et le Tout-puissant qui a rempli mon âme d'amertume, est vivant,
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 Que tout le temps qu'il y aura du souffle en moi, et que l'Esprit de Dieu sera dans mes narines,
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 Mes lèvres ne prononceront rien d'injuste, et ma langue ne dira point de chose fausse.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 A Dieu ne plaise que je vous reconnaisse pour justes! tant que je vivrai je n'abandonnerai point mon intégrité.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 J'ai conservé ma justice, et je ne l'abandonnerai point; et mon cœur ne me reprochera rien en mes jours.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 Qu'il en soit de mon ennemi comme du méchant; et de celui qui se lève contre moi, comme de l'injuste!
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Car quelle sera l'attente de l'hypocrite, lorsque Dieu lui arrachera son âme, s'il s'est adonné à commettre des extorsions?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Le [Dieu] Fort entendra-t-il ses cris, quand la calamité viendra sur lui?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Trouvera-t-il son plaisir dans le Tout-puissant? Invoquera-t-il Dieu en tout temps?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Je vous enseignerai les œuvres du [Dieu] Fort, et je ne vous cacherai point ce qui [est] par-devers le Tout-puissant.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Voilà, vous avez tous vu [ces choses], et comment vous laissez-vous [ainsi] aller à des pensées vaines?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 Ce sera ici la portion de l'homme méchant, que le [Dieu] Fort lui réserve, et l'héritage que les violents reçoivent du Tout-puissant;
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 Si ses enfants sont multipliés, ce sera pour l'épée; et sa postérité n'aura pas même assez de pain.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Ceux qui resteront seront bien ensevelis après leur mort, mais leurs veuves ne les pleureront point.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Quand il entasserait l'argent comme la poussière, et qu'il entasserait des habits comme on amasse de la boue,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 Il les entassera, mais le juste s'en vêtira, et l'innocent partagera l'argent.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Il s'est bâti une maison comme la teigne, et comme le gardien des vignes bâtit sa cabane.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Le riche tombera, et il ne sera point relevé; il ouvrira ses yeux, et il ne trouvera rien.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Les frayeurs l'atteindront comme des eaux; le tourbillon l'enlèvera de nuit.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Le vent d'Orient l'emportera, et il s'en ira; il l'enlèvera, dis-je, de sa place comme un tourbillon.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Le Tout-puissant se jettera sur lui, et ne l'épargnera point; [et étant poursuivi] par sa main, il ne cessera de fuir.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 On battra des mains contre lui, et on sifflera contre lui du lieu qu'il occupait.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Job 27 >