< Job 20 >

1 Alors Tsophar Nahamathite prit la parole, et dit:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 C'est à cause de cela que mes pensées diverses me poussent à répondre, et que cette promptitude est en moi.
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 J'ai entendu la correction dont tu veux me faire honte, mais [mon] esprit [tirera] de mon intelligence la réponse pour moi.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Ne sais-tu pas que de tout temps, [et] depuis que [Dieu] a mis l'homme sur la terre,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 Le triomphe des méchants est de peu de durée, et que la joie de l'hypocrite n'est que pour un moment?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Quand sa hauteur monterait jusqu'aux cieux, et que sa tête atteindrait jusqu'aux nues,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 Il périra pour toujours comme ses ordures; et ceux qui l'auront vu, diront: Où est-il?
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 Il s'en sera envolé comme un songe, et on ne le trouvera plus; et il s'enfuira comme une vision de nuit.
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 L'œil qui l'aura vu ne le verra plus; et son lieu ne le contemplera plus.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 Ses enfants feront la cour aux pauvres; et ses mains restitueront ce qu'il aura ravi par violence.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 Ses os seront pleins de la punition [des péchés] de sa jeunesse, et elle reposera avec lui dans la poudre.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 Si le mal est doux à sa bouche, et s'il le cache sous sa langue;
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 S'il l'épargne, et ne le rejette point, mais le retient dans son palais;
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 Ce qu'il mangera se changera dans ses entrailles en un fiel d'aspic.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 Il a englouti les richesses, mais il les vomira, et le [Dieu] Fort les jettera hors de son ventre.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 Il sucera le venin de l'aspic, et la langue de la vipère le tuera.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 Il ne verra point les ruisseaux des fleuves, ni les torrents de miel et de beurre.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 Il rendra [ce qu'il aura acquis par des] vexations, et il ne l'engloutira point; [il le rendra] selon sa juste valeur, et il ne s'en réjouira point.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Parce qu'il aura foulé les pauvres et les aura abandonnés, il aura ruiné sa maison, bien loin de la bâtir.
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 Certainement il n'en sentira point de contentement en son ventre, et il ne sauvera rien de ce qu'il aura tant convoité.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Il ne lui restera rien à manger, c'est pourquoi il ne s'attendra plus à son bien.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 Après que la mesure de ses biens aura été remplie, il sera dans la misère; toutes les mains de ceux qu'il aura opprimés se jetteront sur lui.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 S'il a eu de quoi remplir son ventre, [Dieu] lui fera sentir l'ardeur de sa colère, et [la] fera pleuvoir sur lui [et] sur sa viande.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 S'il s'enfuit de devant les armes de fer, l'arc d'airain le transpercera.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 Le trait décoché contre lui sortira tout au travers de son corps, et le fer étincelant sortira de son fiel; toute sorte de frayeur marchera sur lui.
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 Toutes les ténèbres seront renfermées dans ses demeures les plus secrètes; un feu qu'on n'aura point soufflé, le consumera; l'homme qui restera dans sa tente sera malheureux.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 Les cieux découvriront son iniquité, et la terre s'élèvera contre lui.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 Le revenu de sa maison sera transporté; tout s'écoulera au jour de la colère de Dieu [contre lui].
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 C'est là la portion que Dieu réserve à l'homme méchant, et l'héritage qu'il aura de Dieu pour ses discours.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”

< Job 20 >