< Job 13 >

1 Voici, mon œil a vu toutes ces choses, [et] mon oreille les a ouïes et entendues.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 Comme vous les savez, je les sais aussi; je ne vous suis pas inférieur.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Mais je parlerai au Tout-puissant, et je prendrai plaisir à dire mes raisons au [Dieu] Fort.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Et certes vous inventez des mensonges; vous êtes tous des médecins inutiles.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 Plût à Dieu que vous demeurassiez entièrement dans le silence; et cela vous serait réputé à sagesse.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Ecoutez donc maintenant mon raisonnement, et soyez attentifs à la défense de mes lèvres:
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Allégueriez-vous des choses injustes, en faveur du [Dieu] Fort, et diriez-vous quelque fausseté pour lui?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Ferez-vous acception de sa personne, si vous plaidez la cause du [Dieu] Fort?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Vous en prendra-t-il bien, s'il vous sonde? vous jouerez-vous de lui, comme on se joue d'un homme [mortel]?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Certainement il vous censurera, si même en secret vous faites acception de personnes.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Sa majesté ne vous épouvantera-t-elle point? et sa frayeur ne tombera-t-elle point sur vous?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Vos discours mémorables sont des sentences de cendre, et vos éminences sont des éminences de boue.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Taisez-vous devant moi, et que je parle; et qu'il m'arrive ce qui pourra.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Pourquoi porté-je ma chair entre mes dents, et tiens-je mon âme entre mes mains?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Voilà, qu'il me tue, je ne laisserai pas d'espérer [en lui]; et je défendrai ma conduite en sa présence.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Et qui plus est, il sera lui-même ma délivrance; mais l'hypocrite ne viendra point devant sa face.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Ecoutez attentivement mes discours, et prêtez l'oreille à ce que je vais vous déclarer.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Voilà, aussitôt que j'aurai déduit par ordre mon droit, je sais que je serai justifié.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Qui est-ce qui veut disputer contre moi? car maintenant si je me tais, je mourrai.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Seulement ne me fais point ces deux choses, [et] alors je ne me cacherai point devant ta face;
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Retire ta main de dessus moi, et que ta frayeur ne me trouble point.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Puis appelle-moi, et je répondrai; ou bien je parlerai, et tu me répondras.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 Combien ai-je d'iniquités et de péchés? Montre-moi mon crime et mon péché.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Pourquoi caches-tu ta face, et me tiens-tu pour ton ennemi?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Déploieras-tu tes forces contre une feuille que le vent emporte? poursuivras-tu du chaume tout sec?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Que tu donnes contre moi des arrêts d'amertume, et que tu me fasses porter la peine des péchés de ma jeunesse?
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Et que tu mettes mes pieds aux ceps, et observes tous mes chemins? et que tu suives les traces de mes pieds?
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Car celui [que tu poursuis de cette manière, ] s'en va par pièces comme du bois vermoulu, et comme une robe que la teigne a rongée.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< Job 13 >