< Jérémie 9 >

1 Plût à Dieu que ma tête fût comme un réservoir d'eau, et que mes yeux fussent une vive fontaine de larmes, et je pleurerais jour et nuit les blessés à mort de la fille de mon peuple!
Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
2 Plût à Dieu que j'eusse au désert une cabane de voyageurs, j'abandonnerais mon peuple, et me retirerais d'avec eux; car ils sont tous des adultères, et une troupe de perfides.
Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
3 Ils ont tendu leur langue, [qui leur a été comme] leur arc pour décocher le mensonge, et ils se sont renforcés dans la terre contre la fidélité, parce qu'ils sont allés de malice en malice, et ne m'ont point reconnu, dit l'Eternel.
“Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
4 Gardez-vous chacun de son intime ami, et ne vous fiez à aucun frère; car tout frère fait métier de supplanter, et tout intime ami va médisant.
“Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
5 Et chacun se moque de son intime ami, et on ne parle point en vérité; ils ont instruit leur langue à dire le mensonge, ils se tourmentent extrêmement pour mal faire.
Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
6 Ta demeure est au milieu de la tromperie; ils refusent à cause de la tromperie de me reconnaître, dit l'Eternel.
Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
7 C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel des armées: voici, je m'en vais les fondre, et je les éprouverai; car comment en agirais-je autrement à l'égard de la fille de mon peuple?
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
8 Leur langue est un trait décoché, elle profère des fraudes; chacun a la paix dans sa bouche avec son intime ami, mais dans son intérieur il lui dresse des embûches.
Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
9 Ne punirais-je point en eux ces choses-là? dit l'Eternel. Mon âme ne se vengerait-elle pas d'une nation qui est telle?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
10 J'élèverai ma voix avec larmes, et je prononcerai à haute voix une lamentation à cause des montagnes, et une complainte à cause des cabanes du désert, parce qu'elles ont été brûlées, de sorte qu'il n'y a personne qui y passe, et qu'on n'y entend plus le cri des troupeaux; les oiseaux des cieux et le bétail s'en sont fuis, ils s'en sont allés.
Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
11 Et je réduirai Jérusalem en monceaux de ruines, elle sera une retraite de dragons, et je détruirai les villes de Juda, tellement qu'il n'y aura personne qui y habite.
“Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
12 Qui est l'homme sage qui entende ceci, et qui est celui à qui la bouche de l'Eternel ait parlé, qui en fasse le rapport, [et qui dise] pourquoi le pays est-il désolé, et brûlé comme un désert, sans que personne y passe?
Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
13 L'Eternel donc a dit: parce qu'ils ont abandonné ma Loi, laquelle je leur avais proposée, et qu'ils n'ont point écouté ma voix, et n'ont point marché selon elle;
Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
14 Mais parce qu'ils ont marché après la dureté de leur cœur, et après les Bahalins; ce que leurs pères leur ont enseigné;
A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
15 C'est pourquoi, ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: voici, je m'en vais donner à manger à ce peuple-ci de l'absinthe, et je leur donnerai à boire de l'eau de fiel.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
16 Je les disperserai parmi les nations que ni eux ni leurs pères n'ont point connues; et j'enverrai après eux l'épée, jusqu’à ce que je les aie consumés.
Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
17 Ainsi a dit l'Eternel des armées: recherchez, et appelez des pleureuses, afin qu'elles viennent, et mandez les femmes sages, et qu'elles viennent;
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
18 Qu'elles se hâtent, et qu'elles prononcent à haute voix une lamentation sur nous, et que nos yeux se fondent en pleurs et que nos paupières fassent ruisseler des larmes.
Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
19 Car une voix de lamentation a été ouïe de Sion, [disant]: comment avons-nous été détruits? Nous sommes fort confus, parce que nous avons abandonné le pays, parce que nos tentes nous ont jetés dehors.
An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
20 C'est pourquoi, vous femmes, écoutez la parole de l'Eternel, et que votre oreille reçoive la parole de sa bouche; et enseignez vos filles à lamenter, et chacune sa compagne à faire des complaintes.
Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
21 Car la mort est montée par nos fenêtres, elle est entrée dans nos palais, pour exterminer les enfants, [tellement qu'il n'y en a plus] dans les rues; et les jeunes gens, [tellement qu'il n'y en a plus] par les places.
Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
22 Dis: ainsi a dit l'Eternel: même les corps morts des hommes seront étendus comme du fumier sur le dessus des champs, et comme une poignée d'épis après les moissonneurs, lesquels personne ne recueille.
Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
23 Ainsi a dit l'Eternel: que le sage ne se glorifie point en sa sagesse; que le fort ne se glorifie point en sa force, et que le riche ne se glorifie point en ses richesses;
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
24 Mais que celui qui se glorifie, se glorifie en ce qu'il a de l'intelligence, et qu'il me connaît; car je suis l'Eternel, qui fais miséricorde, et jugement, et justice sur la terre; parce que je prends plaisir en ces choses-là, dit l'Eternel.
amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
25 Voici, les jours viennent, dit l'Eternel, que je punirai tout circoncis ayant [encore] le prépuce.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
26 L'Egypte, et Juda, et Edom, et les enfants de Hammon, et Moab, et tous ceux qui sont aux bouts des coins, habitant dans le désert; car toutes les nations ont le prépuce, et toute la maison d'Israël a le prépuce du cœur.
Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”

< Jérémie 9 >