< Jérémie 45 >

1 La parole que Jérémie le Prophète dit à Baruc fils de Nérija, quand il écrivait dans un livre ces paroles-là, de la bouche de Jérémie, en la quatrième année de Jéhojakim fils de Josias Roi de Juda, disant:
Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
2 Ainsi a dit l'Eternel, le Dieu d'Israël, touchant toi, Baruc.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
3 Tu as dit: malheur à moi! car l'Eternel a ajouté la tristesse à ma douleur; je me suis lassé dans mon gémissement, et je n'ai point trouvé de repos.
Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
4 Tu lui diras ainsi: ainsi a dit l'Eternel: voici, je m'en vais détruire ce que j'ai bâti, et arracher ce que j'ai planté, [savoir] tout ce pays-ci.
Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
5 Et toi te chercherais-tu des grandeurs? Ne les cherche point; car voici, je m'en vais faire venir du mal sur toute chair, dit l'Eternel; mais je te donnerai ta vie pour butin, dans tous les lieux où tu iras.
Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”

< Jérémie 45 >