< Jérémie 44 >

1 La parole qui fut [adressée] à Jérémie touchant tous les Juifs qui demeuraient au pays d'Egypte, et qui habitaient à Migdol, à Taphnés, à Noph, et au pays de Patros, en disant:
Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
2 Ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: vous avez vu tout le mal que j'ai fait venir sur Jérusalem, et sur toutes les villes de Juda; et voici elles [sont] aujourd'hui un désert, et personne n'y demeure;
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
3 A cause des maux qu'ils ont faits pour m'irriter, en allant faire des encensements pour servir d'autres dieux, lesquels ils n'ont point connus, ni eux, ni vous, ni vos pères.
saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
4 Et je vous ai envoyé tous mes serviteurs les Prophètes, me levant dès le matin, et les envoyant pour vous dire: ne commettez point maintenant cette chose abominable, laquelle je hais.
Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
5 Mais ils n'ont point écouté, et n'ont point incliné leur oreille pour se détourner de leur malice, afin de ne faire point d'encensements à d'autres dieux.
Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
6 C'est pourquoi ma fureur et ma colère s'est répandue sur eux et s'est allumée dans les villes de Juda, et dans les rues de Jérusalem, qui sont réduites en désert, [et] en désolation, comme [il paraît] aujourd'hui.
Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
7 Maintenant donc, ainsi a dit l'Eternel, le Dieu des armées, le Dieu d'Israël: pourquoi faites-vous ce grand mal contre vous-mêmes, pour vous faire retrancher du milieu de Juda, hommes et femmes, petits enfants, et ceux qui tètent, afin qu'on ne vous laisse aucun de reste?
“To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
8 En m'irritant par les œuvres de vos mains, en faisant des encensements à d'autres dieux dans le pays d'Egypte, auquel vous venez d'entrer pour y séjourner, afin que vous soyez retranchés, et que vous soyez en malédiction et en opprobre parmi toutes les nations de la terre?
Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
9 Avez-vous oublié les crimes de vos pères, et les crimes des Rois de Juda, et les crimes de leurs femmes, et vos propres crimes, et les crimes de vos femmes, qu'elles ont commis dans le pays de Juda, et dans les rues de Jérusalem?
Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
10 Jusques à ce jour ils n'ont point été affligés, ils n'ont point eu de crainte, et ils n'ont point marché en ma Loi, ni en mes ordonnances, que je vous ai proposées, et à vos pères aussi.
Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
11 C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: voici, je m'en vais tourner ma face contre vous pour vous nuire, et pour retrancher tout Juda.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
12 Et je prendrai le reste de ceux de Juda qui se sont préparés pour entrer au pays d'Egypte, et y séjourner, et ils seront tous consumés; ils tomberont dans le pays d'Egypte, ils seront consumés par l'épée, et par la famine, depuis le plus petit jusqu’au plus grand; ils mourront par l'épée, et par la famine; et ils seront en exécration, en étonnement, en malédiction, et en opprobre.
Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
13 Et je punirai ceux qui demeurent au pays d'Egypte, comme j'ai puni Jérusalem, par l'épée, par la famine, et par la mortalité.
Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
14 Et il n'y aura personne des restes de Juda d'entre ceux qui sont venus pour demeurer là, [c'est-à-dire], au pays d'Egypte, pour retourner au pays de Juda, auquel ils se promettent de retourner pour y demeurer, qui échappe, et qui y reste; car pas un ne retournera, sinon ceux qui se seront échappés [des autres].
Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
15 Mais tous ceux qui savaient que leurs femmes faisaient des encensements à d'autres dieux, et toutes les femmes qui étaient là en grande compagnie; et tout le peuple qui demeurait dans le pays d'Egypte, à Patros, répondirent à Jérémie, en disant:
Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
16 Quant à la parole que tu nous as dite au Nom de l'Eternel, nous ne t'écouterons point;
“Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
17 Mais nous ferons assurément tout ce qui est sorti de notre bouche en faisant des encensements à la Reine des cieux, et lui faisant des aspersions, comme nous et nos pères, nos Rois, et les principaux d'entre nous avons fait dans les villes de Juda, et dans les rues de Jérusalem, et nous avons eu alors abondamment de pain, nous avons été à notre aise, et nous n'avons point vu de mal.
Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
18 Mais depuis le temps que nous avons cessé de faire des encensements à la Reine des cieux, et de lui faire des aspersions, nous avons eu faute de tout, et nous avons été consumés par l'épée et par la famine.
Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
19 Quand nous faisions des encensements à la Reine des cieux, et quand nous lui faisions des aspersions, lui avons-nous offert à l'insu de nos maris des gâteaux sur lesquels elle était représentée, ou lui avons-nous répandu des aspersions?
Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
20 Alors Jérémie parla à tout le peuple, contre les hommes, et contre les femmes, et contre tout le peuple qui avait fait cette réponse, et leur dit:
Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
21 L'Eternel ne s'est-il pas souvenu des encensements que vous avez faits dans les villes de Juda, et dans les rues de Jérusalem, vous et vos pères, vos Rois et les principaux d'entre vous, et le peuple du pays, et son cœur n'en a-t-il pas été touché?
“Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
22 En sorte que l'Eternel ne l'a pu supporter davantage, à cause de la malice de vos actions, et à cause des abominations que vous avez commises; tellement que votre pays a été réduit en désert, et en étonnement, et en malédiction, sans que personne y habite, comme [il paraît] aujourd'hui.
Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
23 Parce donc que vous avez fait ces encensements, et que vous avez péché contre l'Eternel, et que vous n'avez point écouté la voix de l'Eternel, et n'avez point marché en sa Loi, ni en ses ordonnances, ni en ses témoignages, à cause de cela ce mal vous est arrivé, comme [il paraît] aujourd'hui.
Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
24 Puis Jérémie dit à tout le peuple, et à toutes les femmes: vous tous ceux de Juda, qui êtes au pays d'Egypte, écoutez la parole de l'Eternel.
Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
25 Ainsi a parlé l'Eternel des armées le Dieu d'Israël, en disant: c'est vous, et vos femmes qui ont parlé par votre bouche touchant ce que vous avez accompli de vos mains, en disant: certainement nous accomplirons nos vœux que nous avons voués, en faisant des encensements à la Reine des cieux; et lui faisant des aspersions. Vous avez entièrement accompli vos vœux, et vous les avez effectués très exactement.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
26 C'est pourquoi écoutez la parole de l'Eternel, vous tous ceux de Juda qui demeurez au pays d'Egypte: voici, j'ai juré par mon grand Nom, a dit l'Eternel, que mon Nom ne sera plus réclamé par la bouche d'aucun de Juda, qui dise en tout le pays d'Egypte: le Seigneur l'Eternel est vivant.
Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
27 Voici, je veille contre eux pour [leur] mal, et non pour [leur] bien; et tous les hommes de Juda qui sont au pays d'Egypte seront consumés par l'épée, et par la famine, jusqu’à ce qu'il n'y en ait plus aucun.
Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
28 Et ceux qui seront échappés de l'épée retourneront du pays d'Egypte au pays de Juda en fort petit nombre, et tout le reste de ceux de Juda qui seront entrés au pays d'Egypte pour y séjourner, saura quelle est la parole qui s'accomplira, la mienne, ou la leur.
Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
29 Et ceci vous sera pour signe, dit l'Eternel, que je vous punirai en ce lieu-ci, afin que vous sachiez que mes paroles seront infailliblement accomplies contre vous en mal.
“‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
30 Ainsi a dit l'Eternel: voici, je m'en vais livrer Pharaon-Hophrah Roi d'Egypte en la main de ses ennemis, et en la main de ceux qui cherchent sa vie, comme j'ai livré Sédécias Roi de Juda en la main de Nébucadnetsar Roi de Babylone son ennemi, et qui cherchait sa vie.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”

< Jérémie 44 >