< Jérémie 24 >
1 L'Eternel me fit voir [une vision], et voici deux paniers de figues, posés devant le Temple de l'Eternel, après que Nébucadnetsar Roi de Babylone eut transporté de Jérusalem Jéchonias fils de Jéhojakim, Roi de Juda, et les principaux de Juda, avec les charpentiers et les serruriers, et les eut emmenés à Babylone.
Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
2 L'un des paniers avait de fort bonnes figues, comme sont d'ordinaire les figues qui sont les premières mûres; et l'autre panier avait de fort mauvaises figues, lesquelles on n'aurait pu manger, tant elles étaient mauvaises.
Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
3 Et l'Eternel me dit: que vois-tu, Jérémie? Et je répondis: des figues, de bonnes figues, fort bonnes; et de mauvaises, fort mauvaises, lesquelles on ne saurait manger, tant elles sont mauvaises.
Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
4 Alors la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
5 Ainsi a dit l'Eternel, le Dieu d'Israël: comme ces figues sont bonnes, ainsi je me souviendrai, pour leur faire du bien, de ceux qui ont été transportés de Juda, lesquels j'ai envoyés hors de ce lieu au pays des Caldéens.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
6 Et je mettrai mes yeux sur eux pour leur faire du bien, et je les ferai retourner en ce pays, je les y rétablirai, et je ne les ruinerai plus, je les planterai, et je ne les arracherai point.
Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
7 Et je leur donnerai un cœur pour me connaître, [pour connaître, dis-je], que je suis l'Eternel; et ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu: car ils se retourneront à moi de tout leur cœur.
Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
8 Et comme ces figues sont si mauvaises qu'on n'en peut manger, tant elles sont mauvaises; ainsi certainement, a dit l'Eternel, je rendrai tel Sédécias le Roi de Juda, et les principaux de sa Cour, et le reste de Jérusalem qui sont demeurés dans ce pays, et ceux qui s'habitueront au pays d'Egypte.
“‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
9 Et je les livrerai pour être agités pour leur malheur par tous les Royaumes de la terre, et pour être en opprobre, en proverbe, en raillerie, et en malédiction par tous les lieux où je les aurai chassés.
Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
10 Et j'enverrai sur eux l'épée, la famine, et la mortalité, jusqu’à ce qu'ils soient consumés de dessus la terre que je leur avais donnée, à eux, et à leurs pères.
Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”