< Jérémie 16 >

1 Puis la parole de l'Eternel me fut adressée, en disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Tu ne prendras point de femme, et tu n'auras point de fils ni de filles en ce lieu-ci.
“Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
3 Car ainsi a dit l'Eternel touchant les fils et les filles qui naîtront en ce lieu-ci, et touchant leurs mères qui les auront enfantés, et touchant les pères qui les auront engendrés en ce pays;
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
4 Ils mourront de maladies très douloureuses; ils ne seront point lamentés, ni ensevelis, mais ils seront sur le dessus de la terre comme du fumier, et ils seront consumés par l'épée et par la famine, et leurs corps morts seront pour viande aux oiseaux des cieux, et aux bêtes de la terre.
“Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
5 Même, ainsi a dit l'Eternel: n'entre point en aucune maison de deuil, et ne va point lamenter, ni te condouloir pour eux; car j'ai retiré de ce peuple, dit l'Eternel, ma paix, ma miséricorde, et mes compassions.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
6 Et les grands et les petits mourront en ce pays; ils ne seront point ensevelis, et on ne les pleurera point, et personne ne se fera aucune incision, ni ne se rasera pour eux.
“Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
7 On ne leur distribuera point de [pain] dans le deuil pour consoler quelqu'un d'eux au sujet d'un mort; et on ne leur donnera point à boire de la coupe de consolation pour leur père ou pour leur mère.
Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
8 Aussi tu n'entreras point en aucune maison de festin afin de t'asseoir avec eux pour manger, ou pour boire.
“Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
9 Car ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: voici, je m'en vais faire cesser de ce lieu-ci devant vos yeux et en vos jours, la voix de joie et la voix d'allégresse, la voix de l'époux et la voix de l'épouse.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
10 Et il arrivera que quand tu auras prononcé à ce peuple toutes ces paroles-là, ils te diront: pourquoi l'Eternel a-t-il prononcé tout ce grand mal contre nous? et quelle est notre iniquité, et quel [est] notre péché que nous avons commis contre l'Eternel notre Dieu?
“Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
11 Et tu leur diras: parce que vos pères m'ont abandonné, dit l'Eternel, et sont allés après d'autres dieux, et les ont servis, et se sont prosternés devant eux, et m'ont abandonné, et n'ont point gardé ma Loi,
Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
12 Et que vous avez encore fait pis que vos pères; car voici, chacun de vous marche après la dureté de son cœur mauvais, afin de ne m'écouter point;
Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
13 A cause de cela je vous transporterai de ce pays en un pays que vous n'avez point connu, ni vous ni vos pères; et là vous serez asservis jour et nuit à d'autres dieux, parce que je ne vous aurai point fait de grâce.
Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
14 Néanmoins voici, les jours viennent, dit l'Eternel, qu'on ne dira plus: l'Eternel [est] vivant qui a fait remonter les enfants d'Israël du pays d'Egypte;
“Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
15 Mais, l'Eternel est vivant qui a fait remonter les enfants d'Israël du pays de l'Aquilon, et de tous les pays auxquels il les avait chassés; après que je les aurai ramenés dans leur pays, lequel j'ai donné à leurs pères.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
16 Voici, je m'en vais mander à plusieurs Pêcheurs, dit l'Eternel, et ils les pêcheront; et ensuite je m'en vais mander à plusieurs Veneurs, qui les chasseront par toutes les montagnes, et par tous les coteaux, et par tous les trous des rochers.
“Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
17 Car mes yeux sont sur tout leur train, lequel n'est point caché devant moi; ni leur iniquité n'est point celée devant mes yeux.
Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
18 Mais premièrement je leur rendrai le double de leur iniquité et de leur péché, à cause qu'ils ont souillé mon pays par leurs victimes abominables, et qu'ils ont rempli mon héritage de leurs abominations.
Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
19 Eternel, qui es ma force et ma puissance, et mon refuge au jour de la détresse, les nations viendront à toi des bouts de la terre, et diront: certes nos pères ont hérité le mensonge et la vanité, et les choses auxquelles il n'y a point de profit.
Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
20 L'homme se fera-t-il bien des dieux? qui toutefois ne sont point dieux.
Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
21 C'est pourquoi, voici, je vais leur faire connaître à cette fois, je vais leur faire connaître ma main et ma force, et ils sauront que mon Nom est l'Eternel.
“Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.

< Jérémie 16 >