< Isaïe 38 >
1 En ces jours-là Ezéchias fut malade à la mort, et Esaïe le Prophète fils d'Amots vint vers lui, et lui dit; ainsi a dit l'Eternel; dispose de ta maison, car tu t'en vas mourir, et tu ne vivras plus.
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
2 Alors Ezéchias tourna sa face contre la muraille, et fit sa prière à l'Eternel.
Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
3 Et dit; souviens-toi maintenant je te prie, ô Eternel! comment j'ai marché devant toi en vérité et en intégrité de cœur, et comment j'ai fait ce qui t'était agréable; et Ezéchias pleura abondamment.
“Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 Or la parole de l'Eternel fut adressée à Esaïe, en disant;
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
5 Va, et dis à Ezéchias ainsi a dit l'Eternel, le Dieu de David ton père; j'ai exaucé ta prière, j'ai vu tes larmes; voici, je m'en vais ajouter quinze années à tes jours.
“Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
6 Et je te délivrerai de la main du Roi des Assyriens, toi et cette ville, et je garantirai cette ville.
Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
7 Et ce signe t'est donné par l'Eternel, [pour faire voir] que l'Eternel accomplira cette parole qu'il a prononcée;
“‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
8 Voici, je m'en vais faire retourner l'ombre des degrés par lesquels elle est descendue au cadran d'Achaz, de dix degrés en arrière avec le soleil; et le soleil retourna de dix degrés par les degrés par lesquels il était descendu.
Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
9 Or c'est ici l'Ecrit d'Ezéchias Roi de Juda, touchant ce qu'il fut malade, et qu'il fut guéri de sa maladie.
Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
10 J'avais dit dans le retranchement de mes jours; je m'en irai aux portes du sépulcre, je suis privé de ce qui restait de mes années. (Sheol )
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
11 J'avais dit; je ne contemplerai plus l'Eternel, l'Eternel, dans la terre des vivants; je ne verrai plus personne avec les habitants du monde.
Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
12 Ma durée s'en est allée, et a été transportée d'avec moi, comme une cabane de berger; j'ai tranché ma vie comme le tisserand [coupe sa toile]; il me coupera dès les pesnes: du matin au soir tu m'auras enlevé.
Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
13 Je me proposais jusqu'au matin qu'il était comme un lion, qu'il briserait ainsi tous mes os; du matin au soir tu m'auras enlevé.
Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
14 Je grommelais comme la grue, et [comme] l'hirondelle; je gémissais comme le pigeon; mes yeux défaillaient à force de regarder en haut; Seigneur, on me fait force, sois mon garant.
Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
15 Que dirai-je? il m'a parlé; et lui même l'a fait; je m'en irai tout doucement, tous les ans de ma vie, dans l'amertume de mon âme.
Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
16 Seigneur, par ces choses-là on a la vie, et dans tout [ce qui est] en ces choses consiste la vie de mon esprit; ainsi tu me rétabliras, et me feras revivre.
Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
17 Voici, dans ma paix une grande amertume m'était survenue, mais tu as embrassé ma personne, afin qu'elle ne tombât point dans la fosse de la pourriture; parce que tu as jeté tous mes péchés derrière ton dos.
Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
18 Car le sépulcre ne te célébrera point, la mort ne te louera point; ceux qui descendent en la fosse, ne s'attendent plus à ta vérité. (Sheol )
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
19 Mais le vivant, le vivant, est celui qui te célébrera, comme moi aujourd'hui; le père conduira les enfants à la connaissance de ta vérité.
Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
20 L'Eternel m'est venu délivrer, et à cause de cela nous jouerons sur les instruments mes cantiques tous les jours de notre vie, dans la maison de l'Eternel.
Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
21 Or Esaïe avait dit; qu'on prenne une masse de figues sèches, et qu'on en fasse une emplâtre sur l'ulcère, et il guérira.
Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
22 Et Ezéchias avait dit; quel est le signe que je monterai en la maison de l'Eternel?
Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”