< Isaïe 13 >

1 La charge de Babylone, qu'Esaïe fils d'Amots a vue.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Elevez l'enseigne sur la haute montagne, élevez la voix vers eux, remuez la main, et qu'on entre dans les portes des magnifiques.
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 C'est moi qui ai donné charge à ceux qui me sont dévoués, et j'ai appelé pour [exécuter] ma colère mes hommes forts, qui s'égayent à cause de ma grandeur.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 Il y a sur les montagnes un bruit d'une multitude, tel qu'est celui d'un grand peuple, un bruit d'un son éclatant des Royaumes des nations assemblées; l'Eternel des armées fait la revue de l'armée pour le combat.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 L'Eternel et les instruments de son indignation viennent d'un pays éloigné, du bout des cieux, pour détruire tout le pays.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Hurlez; car la journée de l'Eternel est proche, elle viendra comme un dégât [fait] par le Tout-Puissant.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 C'est pourquoi toutes les mains deviendront lâches, et tout cœur d'homme se fondra.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 Ils seront épouvantés, les détresses et les douleurs les saisiront, ils seront en travail comme celle qui enfante, chacun s'étonnera [regardant] vers son prochain, leurs visages seront comme des visages enflammés.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Voici, la journée de l'Eternel vient, elle est cruelle, elle n'est que fureur et ardeur de colère, pour réduire le pays en désolation, et il en exterminera les pécheurs.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 Même les étoiles des cieux et leurs astres ne feront point luire leur clarté; le Soleil s'obscurcira quand il se lèvera, et la Lune ne fera point resplendir sa lueur.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 Je punirai le monde habitable à cause de sa malice, et les méchants à cause de leur iniquité; je ferai cesser l'arrogance de ceux qui se portent fièrement, et j'abaisserai la hauteur de ceux qui se font redouter.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 Je ferai qu'un homme sera plus précieux que le fin or; et une personne, plus que l'or d'Ophir.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 C'est pourquoi je ferai crouler les cieux, et la terre sera ébranlée de sa place, à cause de la fureur de l'Eternel des armées, et à cause du jour de l'ardeur de sa colère.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 Et [chacun] sera comme un chevreuil qui est chassé, et comme une brebis que personne ne retire; chacun tournera visage vers son peuple, et chacun s'enfuira vers son pays.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Quiconque sera trouvé, sera transpercé; et quiconque s'y sera joint, tombera par l'épée.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Et leurs petits enfants seront écrasés devant leurs yeux, leurs maisons seront pillées, et leurs femmes violées.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Voici, je vais susciter contre eux les Mèdes, qui ne feront aucune estime de l'argent, et qui ne s'arrêteront point à l'or.
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 Leurs arcs écraseront les jeunes gens, et ils n'auront point de pitié du fruit du ventre, leur œil n'épargnera point les enfants.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 Ainsi Babylone, la noblesse des Royaumes, l'excellence de l'orgueil des Chaldéens, sera comme quand Dieu renversa Sodome et Gomorrhe.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 Elle ne sera point habitée à jamais, elle ne sera point habitée de génération en génération, même les Arabes n'y dresseront point leurs tentes, ni les bergers n'y mettront point leurs parcs.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Mais les bêtes sauvages des déserts y auront leurs repaires; et leurs maisons seront remplies de fouines, les chats-huants y habiteront, et les chouettes y sauteront.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 Et [les bêtes sauvages des] Iles s'entre-répondront les unes aux autres dans ses palais désolés, et les dragons dans ses châteaux de plaisance; son temps est même prêt à venir, et ses jours ne seront point prolongés.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Isaïe 13 >