< Isaïe 10 >

1 Malheur à ceux qui font des ordonnances d'iniquité, et qui dictent l'oppression qu'on leur a dictée.
Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
2 Pour enlever aux chétifs de leur droit, et pour ravir le droit des affligés de mon peuple, afin d'avoir les veuves pour leur butin, et de piller les orphelins.
don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
3 Et que ferez-vous au jour de la visitation, et de la ruine éclatante qui viendra de loin? vers qui recourrez-vous pour avoir du secours, et où laisserez-vous votre gloire?
Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
4 Sans qu'aucun soit courbé sous les prisonniers, ils tomberont même sous ceux qui auront été tués. Malgré tout cela il ne fera point cesser sa colère, mais sa main sera encore étendue.
Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
5 Malheur à Assur, la verge de ma colère; quoique le bâton qui est en leur main [soit] mon indignation.
“Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
6 Je l'enverrai contre la nation hypocrite, et je le dépêcherai contre le peuple de ma fureur, afin qu'il fasse un grand butin, et un grand pillage, et qu'il le foule comme la boue des rues.
Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
7 Mais il ne l'estimera pas ainsi, et son cœur ne le pensera pas ainsi; mais [il aura] en son cœur de détruire et d'exterminer beaucoup de nations.
Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
8 Car il dira; mes Princes ne sont-ils pas autant de Rois?
Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
9 Calno, n'est-elle pas comme Carchémis? Hamath, n'est-elle pas comme Arpad? et Samarie, n'est-elle pas comme Damas?
‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
10 Ainsi que ma main a soumis les Royaumes [qui avaient] des idoles, et desquels les images taillées [valaient plus] que [celles] de Jérusalem et de Samarie;
Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
11 Ne ferai-je pas aussi à Jérusalem et à ses dieux, comme j'ai fait à Samarie et à ses idoles?
ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
12 Mais il arrivera que quand le Seigneur aura achevé toute son œuvre dans la montagne de Sion et à Jérusalem, j'examinerai le fruit de la grandeur du cœur du Roi d'Assyrie, et la gloire de la fierté de ses yeux.
Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
13 Parce qu'il aura dit; je l'ai fait par la force de ma main, et par ma sagesse, car je suis intelligent; j'ai ôté les bornes des peuples, et j'ai pillé ce qu'ils avaient de plus précieux, et comme puissant j'ai fait descendre ceux qui étaient assis.
Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
14 Et ma main a trouvé comme un nid les richesses des peuples; et ainsi qu'on rassemble les œufs délaissés, ainsi ai-je rassemblé toute la terre, et il n'y a eu personne qui ait remué l'aile, ou qui ait ouvert le bec, ou qui ait grommelé.
Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
15 La cognée se glorifiera-t-elle contre celui qui en coupe? ou la scie se magnifiera-t-elle contre celui qui la remue? comme si la verge se remuait contre ceux qui la lèvent en haut, et que le bâton s'élevât, [comme] s'il n'était pas du bois.
Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
16 C'est pourquoi le Seigneur, l'Eternel des armées enverra la maigreur sur ses hommes gras, et par le dessous de sa gloire il allumera un embrasement, tel que l'embrasement d'un feu.
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
17 Car la lumière d'Israël sera un feu, et son Saint sera une flamme, qui embrasera et consumera ses épines et ses ronces tout en un jour.
Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
18 Et il consumera la gloire de sa forêt, et de son Carmel, depuis l'âme jusqu'à la chair; et il en sera comme quand celui qui porte l'étendart est défait.
Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
19 Et le reste des arbres de sa forêt seront aisés à compter, tellement qu'un enfant les mettrait bien en écrit.
Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
20 Et il arrivera en ce jour-là que le résidu d'Israël, et ceux qui seront réchappés de la maison de Jacob, ne s'appuieront plus sur celui qui les frappait, mais ils s'appuieront en vérité sur l'Eternel, le Saint d'Israël.
A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
21 Le résidu sera converti, le résidu, [dis-je], de Jacob [sera converti] au [Dieu] Fort et puissant.
Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
22 Car, ô Israël! quand ton peuple serait comme le sablon de la mer, un résidu en sera converti, [mais] la consomption déterminée fera déborder la justice.
Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
23 Car le Seigneur l'Eternel des armées s'en va faire une consomption, même déterminée, au milieu de toute la terre.
Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
24 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel des armées; mon peuple qui habites dans Sion, ne crains point le Roi d'Assyrie; il te frappera de la verge, et il lèvera son bâton sur toi à la manière d'Egypte.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
25 Mais encore un peu de temps, un peu de temps, et [mon] indignation sera consommée, et ma colère sera à leur destruction.
Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
26 Et l'Eternel des armées lèvera sur lui un fouet, [qui sera] comme la plaie de Madian au rocher d'Horeb; et [comme] son bâton sur la mer, lequel il élèvera aussi comme contre les Egyptiens.
Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
27 Et il arrivera en ce jour-là, que son fardeau sera ôté de dessus ton épaule, et son joug de dessus ton cou; et le joug sera rompu à cause de l'onction.
A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
28 Il est venu à Hajath, il est passé à Migron, et il a mis son bagage à Michmas.
Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
29 Ils ont passé le gué; ils ont fait leur gîte à Guébah, Rama s'est effrayée, Guibha-Saül s'en est fuie.
Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
30 Fille de Gallim, élève ta voix, pauvre Hanathoth, fais-toi ouïr vers Laïs.
Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
31 Madména s'est écartée, les habitants de Guébim s'en sont fuis en foule.
Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
32 Encore un jour, il s'arrêtera à Nob; il lèvera sa main [contre] la montagne de la fille de Sion, [contre] le coteau de Jérusalem.
A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
33 Voici, le Seigneur, l'Eternel des armées ébranchera les rameaux avec force, et ceux qui sont les plus haut élevés, seront coupés; et les haut montés seront abaissés.
Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
34 Et il taillera avec le fer les lieux les plus épais de la forêt, et le Liban tombera avec impétuosité.
Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.

< Isaïe 10 >