< Osée 4 >
1 Enfants d'Israël, écoutez la parole de l'Eternel; car l'Eternel a un procès avec les habitants du pays; parce qu'il n'y a point de vérité, ni de miséricorde, ni de connaissance de Dieu au pays.
Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
2 Il n'y a qu'exécration, que mensonge, que meurtre, que larcin et qu'adultère; ils se sont entièrement débordés, et un meurtre touche l'autre.
Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
3 C'est pourquoi le pays sera en deuil, et tout homme qui y habite sera dans la langueur, avec les bêtes des champs, et les oiseaux des cieux; même les poissons de la mer périront.
Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
4 Quoi qu'il en soit, qu'on ne plaide avec personne, et qu'on ne reprenne personne; car, quant à ton peuple, ce sont autant de gens qui disputent avec le Sacrificateur.
“Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
5 Tu tomberas donc en plein jour, et le prophète aussi tombera avec toi de nuit, et j'exterminerai ta mère.
Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
6 Mon peuple est détruit à cause qu'il est sans science. Parce que tu as rejeté la science, je te rejetterai, afin que tu ne m'exerces plus la sacrificature. Puisque tu as oublié la Loi de ton Dieu, moi aussi j'oublierai tes enfants.
mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
7 A mesure qu'ils se sont accrus ils ont péché contre moi: je changerai leur gloire en ignominie.
Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
8 Ils mangent les péchés de mon peuple, et ne demandent rien que son iniquité.
Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
9 C'est pourquoi le Sacrificateur sera [traité] comme le peuple, et je le visiterai selon son train, et je lui rendrai selon ses actions.
Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
10 Et ils mangeront, mais ils ne seront point rassasiés; ils se prostitueront, mais ils ne multiplieront point; parce qu'ils ont abandonné l'Eternel, pour ne s'y tenir point.
“Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
11 La luxure, et le vin, et le moût, ôtent l'entendement.
ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
12 Mon peuple demande avis à son bois, et son bâton lui répond: car l'esprit de fornication [les] a fait errer, et ils ont commis adultère se détournant de leur Dieu.
Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
13 Ils sacrifient sur le sommet des montagnes, et font des parfums sur les coteaux, sous les chênes, sous les peupliers, et sous les ormes, parce que leur ombre est bonne; c'est pourquoi vos filles se prostitueront, et les femmes de vos fils commettront adultère.
Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
14 Je ne ferai point punition de vos filles quand elles se seront abandonnées, ni des femmes de vos fils, quand elles auront commis adultère; à cause qu'ils se séparent avec les prostituées, et qu'ils sacrifient avec les femmes débauchées; ainsi le peuple qui est sans intelligence, sera ruiné.
“Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
15 Si tu commets adultère, ô Israël! [au moins] que Juda ne se rende point coupable; n'entrez donc point dans Guilgal, et ne montez point à Beth-aven, et ne jurez point; l'Eternel est vivant.
“Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
16 Parce qu'Israël a été revêche comme une génisse revêche, l'Eternel les paîtra maintenant comme des agneaux dans des lieux spacieux.
Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
17 Ephraïm s'est associé aux idoles; abandonne-le.
Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
18 Leur breuvage est devenu aigre; ils n'ont fait que se prostituer; ils n'aiment qu'à [dire], apportez; ce n'est qu'ignominie que ses protecteurs.
Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
19 Le vent l'a enserré dans ses ailes, et ils auront honte de leurs sacrifices.
Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.