< Osée 2 >

1 Appelez vos frères Hammi, et vos sœurs Ruhama.
“Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
2 Plaidez, plaidez avec votre mère, car elle n'[est] point ma femme, et aussi ne suis-je point son mari; et qu'elle ôte ses prostitutions de devant elle, et ses adultères de son sein.
“Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
3 De peur que je ne manifeste sa nudité, que je ne la remette dans l'état où elle était le jour qu'elle naquit, que je ne la réduise en désert, et que je ne la fasse être comme une terre sèche, et ne la fasse mourir de soif.
In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
4 Et que je n'use point de miséricorde envers ses enfants, car ce sont des enfants de prostitution.
Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
5 Parce que leur mère s'est prostituée, celle qui les a conçus s'est déshonorée, car elle a dit: Je m'en irai après ceux que j'aime, qui me donnent mon pain et mes eaux, ma laine, et mon lin, mon huile, et mes boissons.
Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
6 C'est pourquoi, voici, je boucherai d'épines ton chemin, et je ferai une cloison de pierres, en sorte qu'elle ne trouvera point ses sentiers.
Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
7 Elle ira donc vers ceux dont elle recherche l'amitié; mais elle ne les atteindra point; elle les cherchera, mais elle ne les trouvera point; et elle dira: Je m'en irai et retournerai à mon premier mari, car alors j'étais mieux que je ne suis maintenant.
Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
8 Mais elle n'a point connu que c'était moi qui lui avais donné le froment, et le vin, et l'huile, et qui lui avais multiplié l'argent et l'or dont ils ont fait un Bahal.
Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
9 C'est pourquoi je viendrai à reprendre mon froment en son temps, et mon vin en sa saison, et je retirerai ma laine et mon lin qui couvraient sa nudité.
“Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
10 Et maintenant je découvrirai sa turpitude devant les yeux de ceux qui l'aiment, et personne ne la délivrera de ma main.
Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
11 Je ferai cesser toute sa joie, ses fêtes, ses nouvelles lunes, ses Sabbats, et toutes ses solennités.
Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
12 Et je gâterai ses vignobles, et ses figuiers, desquels elle a dit: Ce sont ici mes salaires que ceux qui m'aiment m'ont donnés; et je les réduirai en forêt, et les bêtes des champs les dévoreront.
Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
13 Et je visiterai sur elle les jours des Bahalins, durant lesquels elle leur faisait des parfums, et se parait de ses bagues et de ses joyaux, et s'en allait après ceux qui l'aimaient, et m'oubliait, dit l'Eternel.
Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
14 Néanmoins, voici, je l'attirerai après que je l'aurai promenée par le désert, et je lui parlerai selon son cœur.
“Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
15 Et je lui donnerai ses vignes, depuis ce lieu-là, et la vallée de Hachor, pour l'entrée de son attente, et elle y chantera comme au temps de sa jeunesse, et comme lorsqu'elle remonta du pays d'Egypte.
A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
16 Et il arrivera en ce jour-là, dit l'Eternel, que tu m'appelleras, Mon mari, et que tu ne m'appelleras plus, Mon Bahal.
“A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
17 Car j'ôterai de sa bouche les noms des Bahalins, et on n'en fera plus mention par leur nom.
Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
18 Aussi en ce temps-là je traiterai pour eux une alliance avec les bêtes des champs, et avec les oiseaux des cieux, et avec les reptiles de la terre; et je briserai [et j'ôterai] du pays, l'arc, et l'épée, et la guerre, et je les ferai dormir en sûreté.
A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
19 Et je t'épouserai pour moi à toujours; je t'épouserai, dis-je, pour moi, en justice, et en jugement, et en gratuité, et en compassions.
Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
20 Même je t'épouserai en fermeté, et tu connaîtras l'Eternel.
Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
21 Et il arrivera en ce temps-là que je répondrai, dit l'Eternel, que je répondrai aux cieux, et les cieux répondront à la terre.
“A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
22 Et la terre répondra au froment, au bon vin, et à l'huile; et eux répondront à Jizréhel.
ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
23 Puis je la sèmerai pour moi en la terre, et je ferai miséricorde à Lo-ruhama; et je dirai à Lo-hammi, tu es mon peuple; et il me dira, mon Dieu.
Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”

< Osée 2 >