< Genèse 7 >

1 Et l'Eternel dit à Noé: Entre, toi et toute ta maison, dans l'arche; car je t'ai vu juste devant moi en ce temps-ci.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 Tu prendras de toutes les bêtes nettes sept de chaque espèce, le mâle et sa femelle; mais des bêtes qui ne sont point nettes, un couple, le mâle et la femelle;
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 [Tu prendras] aussi des oiseaux des cieux sept de chaque espèce, le mâle et sa femelle; afin d'en conserver la race sur toute la terre.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 Car dans sept jours je ferai pleuvoir sur la terre pendant quarante jours et quarante nuits; et j'exterminerai de dessus la terre toute chose qui subsiste, laquelle j'ai faite.
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Et Noé fit selon tout ce que l'Eternel lui avait commandé.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 Or Noé était âgé de six cents ans quand le déluge des eaux vint sur la terre.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 Noé donc entra, et avec lui ses fils, sa femme, et les femmes de ses fils, dans l'arche, à cause des eaux du déluge.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 Des bêtes nettes, et des bêtes qui ne sont point nettes, et des oiseaux, et de tout ce qui se meut sur la terre.
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 Elles entrèrent deux à deux vers Noé dans l'arche, le mâle et la femelle, comme Dieu avait commandé à Noé.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 Et il arriva qu'au septième jour les eaux du déluge furent sur la terre.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 En l'an six cent de la vie de Noé au second mois, le dix-septième jour du mois, en ce jour-là toutes les fontaines du grand abîme furent rompues, et les bondes des cieux furent ouvertes.
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 Et la pluie tomba sur la terre pendant quarante jours et quarante nuits.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 En ce même jour Noé, et Sem, Cam, et Japheth, fils de Noé, entrèrent dans l'arche, avec la femme de Noé, et les trois femmes de ses fils avec eux.
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 Eux, et toutes les bêtes selon leur espèce, et tout bétail selon son espèce, et tous les reptiles qui se meuvent sur la terre, selon leur espèce, et tous les oiseaux, selon leur espèce; [et] tout petit oiseau ayant des ailes, de quelque sorte que ce soit.
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 Il vint donc de toute chair qui a en soi esprit de vie, par couples à Noé, dans l'arche.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 Le mâle, dis-je, et la femelle de toute chair y vinrent, comme Dieu lui avait commandé; puis l'Eternel ferma l'arche sur lui.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 Et le déluge vint pendant quarante jours sur la terre; et les eaux crurent, et élevèrent l'arche, et elle fut élevée au-dessus de la terre.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 Et les eaux se renforcèrent, et s'accrurent fort sur la terre, et l'arche flottait au-dessus des eaux.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 Les eaux donc se renforcèrent extraordinairement sur la terre, et toutes les plus hautes montagnes qui sont sous tous les cieux, en furent couvertes.
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 Les eaux se renforcèrent de quinze coudées par-dessus, et les montagnes en furent couvertes.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 Et toute chair qui se mouvait sur la terre expira, tant des oiseaux que du bétail, des bêtes à quatre pieds, et de tous les reptiles qui se traînent sur la terre, et tous les hommes.
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 Toutes les choses qui étaient sur le sec, ayant respiration de vie en leurs narines, moururent.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 Tout ce donc qui subsistait sur la terre fut donc exterminé, depuis les hommes jusques aux bêtes, jusques aux reptiles, et jusques aux oiseaux des cieux; ils furent, dis-je, exterminés de dessus la terre; mais seulement Noé, et ce qui était avec lui dans l'arche, demeura de reste.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 Et les eaux se maintinrent sur la terre durant cent cinquante jours.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.

< Genèse 7 >

The Great Flood
The Great Flood