< Genèse 10 >
1 Or ce sont ici les générations des enfants de Noé, Sem, Cam et Japheth; auxquels naquirent des enfants après le déluge.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 Les enfants de Japheth sont Gomer, Magog, Madaï, Javan, Tubal, Mésech, et Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 Et les enfants de Gomer, Askénaz, Riphath, et Thogarma.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 Et les enfants de Javan, Elisa, Tarsis, Kittim, et Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 De ceux-là furent divisées les Iles des nations par leurs terres, chacun selon sa langue, selon leurs familles, entre leurs nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 Et les enfants de Cam sont Cus, Mitsraïm, Put, et Canaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 Et les enfants de Cus: Séba, Havila, Sabtah, Rahma, et Sebtéca. Et les enfants de Rahma, Séba, et Dédan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Cus engendra aussi Nimrod, qui commença d'être puissant sur la terre.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 Il fut un puissant chasseur devant l'Eternel; c'est pourquoi l'on a dit: Comme Nimrod, le puissant chasseur devant l'Eternel.
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 Et le commencement de son règne fut Babel, Erec, Accad, et Calné au pays de Sinhar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 De ce pays-là sortit Assur, et il bâtit Ninive, et les rues de la ville, et Calah,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 Et Résen, entre Ninive et Calah, qui est une grande ville.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 Mitsraïm engendra Ludim, Hanamim, Léhabim, Naphtuhim.
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 Pathrusim, Chasluhim, desquels sont issus les Philistins, et Caphtorim.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Et Canaan engendra Sidon, son fils aîné, et Heth,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 Les Jébusiens, les Amorrhéens, les Guirgasiens,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 Les Héviens, les Harkiens, et les Siniens,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 Les Arvadiens, les Tsémariens, et les Hamathiens. Et ensuite les familles des Cananéens se sont dispersées.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 Et les limites des Cananéens furent depuis Sidon, quand on vient vers Guérar, jusqu'à Gaza, en tirant vers Sodome et Gomorrhe, Adma, et Tséboïm, jusqu'à Lésa.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 Ce sont là les enfants de Cam selon leurs familles [et leurs] langues, en leurs pays, et en [leurs] nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 Et il naquit des enfants à Sem, père de tous les enfants d'Héber, et frère de Japheth, [qui était] le plus grand.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 Et les enfants de Sem sont Hélam, Assur, Arpacsad, Lud, et Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 Et les enfants d'Aram, Hus, Hul, Guéther et Mas.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Et Arpacsad engendra Sélah, et Sélah engendra Héber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 Et à Héber naquirent deux fils: le nom de l'un fut Péleg, parce qu'en son temps la terre fut partagée; et le nom de son frère fut Joktan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Et Joktan engendra Almodad, Séleph, Hatsarmaveth, et Jérah.
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
29 Ophir, Havila, et Jobab. Tous ceux-là sont les enfants de Joktan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 Et leur demeure était depuis Mésa, quand on vient en Séphar, montagne d'Orient.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 Ce sont là les enfants de Sem, selon leurs familles [et] leurs langues, en leurs pays, et en [leurs] nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 Telles sont les familles des enfants de Noé, selon leurs lignées en leurs nations; et de ceux-là ont été divisées les nations sur la terre après le déluge.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.