< Esdras 1 >

1 La première année donc de Cyrus Roi de Perse, afin que la parole de l'Eternel, prononcée par Jérémie, fût accomplie, l'Eternel excita l'esprit de Cyrus, Roi de Perse, qui fit publier dans tout son Royaume, et même par Lettres, en disant:
A shekara ta farko ta mulkin sarkin Farisa, wato, sarki Sairus, domin a cika maganar Ubangiji da aka yi ta bakin Irmiya, sai Ubangiji ya taɓa zuciyar Sairus sarkin Farisa ya yi shela a duk fāɗin ƙasarsa, ya kuma rubuta cewa,
2 Ainsi a dit Cyrus, Roi de Perse: L'Eternel le Dieu des cieux m'a donné tous les Royaumes de la terre, et lui-même m'a ordonné de lui bâtir une maison à Jérusalem, qui est en Judée.
“Ga abin da Sairus sarkin Farisa yake shela, “‘Ubangiji Allah na sama ya ba ni iko in yi mulkin duniya duka, ya kuma zaɓe ni in gina masa haikali a Urushalima cikin Yahuda.
3 Qui est-ce d'entre vous de tout son peuple [qui s'y veuille employer?] Que son Dieu soit avec lui, et qu'il monte à Jérusalem, qui est en Judée, et qu'il rebâtisse la maison de l'Eternel le Dieu d'Israël; c'est le Dieu qui habite à Jérusalem.
Duk wanda yake nasa a cikinku bari Allahnsa yă kasance tare da shi, bari yă tafi Urushalima cikin Yahuda yă gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila, Allah wanda yake a Urushalima.
4 Et quant à tous ceux qui demeureront en arrière, de quelque lieu que ce soit où ils fassent leur séjour, que les gens du lieu où ils demeurent, les soulagent d'argent, d'or, de biens, et de montures, outre ce qu'on offrira volontairement pour la maison du Dieu qui [habite] à Jérusalem.
Duk inda akwai mutumin Yahuda da ya rage, sai mutanen da suke zama kusa da shi, su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da kuma dabbobi, tare da kyautai na yardar rai saboda Gidan Allah wanda yake a Urushalima.’”
5 Alors les Chefs des pères de Juda, de Benjamin, des Sacrificateurs et des Lévites, se levèrent pour conduire tous ceux dont Dieu réveilla l'esprit, afin de remonter pour rebâtir la maison de l'Eternel, qui habite à Jérusalem.
Sai shugabannin zuriyar Yahuda da na Benyamin, da firistoci da Lawiyawa, duk wanda Allah ya taɓa zuciyarsa, suka shirya don su je su gina haikalin Ubangiji a Urushalima.
6 Et tous ceux qui étaient à l'entour d'eux les encouragèrent, leur fournissant des vaisseaux d'argent, et d'or, des biens, des montures, et des choses exquises, outre tout ce qu'on offrit volontairement.
Dukan maƙwabtansu kuwa suka taimake su da gudummawa na kayan azurfa da na zinariya, da kaya, da dabbobi, da kuma kyautai masu daraja bisa bayarwar yardar rai da suka yi.
7 Et le Roi Cyrus fit prendre les vaisseaux de la maison de l'Eternel, que Nébucadnetsar avait tirés de Jérusalem, et qu'il avait mis dans la maison de son Dieu.
Sai sarki Sairus ya fitar da kayan da suke na haikalin Ubangiji waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya sa a haikalin allahnsa.
8 Et Cyrus, Roi de Perse, les fit sortir par Mithredath, le trésorier, qui les livra par compte à Sesbatsar, Prince de Juda.
Sairus sarkin Farisa ya sa Mitredat ma’aji ya ƙirga su a gaban Sheshbazzar ɗan sarkin Yahuda.
9 Et c'est ici leur nombre, trente bassins d'or, mille bassins d'argent, vingt et neuf couteaux,
Ga lissafin kayan. Manyan kwanonin zinariya guda 30 Manyan kwanonin azurfa guda 1,000 Wuƙaƙe guda 29
10 Trente plats d'or, quatre cent et dix plats d'argent du second ordre, et d'autres ustensiles par milliers.
Waɗansu kwanonin zinariya guda 30 Waɗansu kwanonin azurfa guda 410 da waɗansu kayayyaki guda 1,000
11 Tous les ustensiles d'or et d'argent étaient cinq mille quatre cents. Sesbatsar les fit tous rapporter, quand on fit remonter de Babylone à Jérusalem le peuple qui en avait été transporté.
Dukan kayayyakin zinariya da na azurfa sun kai 5,400. Sheshbazzar ya kawo kayayyakin nan duka tare da shi lokacin da kamammun suka hauro daga Babilon zuwa Urushalima.

< Esdras 1 >