< Esdras 10 >

1 Et comme Esdras priait, et faisait cette confession, pleurant, et étant prosterné en terre devant la maison de Dieu, une fort grande multitude d'hommes, et de femmes, et d'enfants de ceux d'Israël, s'assembla vers lui; et le peuple pleura abondamment.
Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
2 Alors Sécania fils de Jéhiël, d'entre les enfants de Hélam, prit la parole, et dit à Esdras: Nous avons péché contre notre Dieu, en ce que nous avons pris des femmes étrangères d'entre les peuples de ce pays; mais maintenant il y a espérance pour Israël en ceci.
Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
3 C'est pourquoi traitons maintenant [cette] alliance avec notre Dieu, que nous ferons sortir toutes les femmes, et tout ce qui est né d'elles, selon le conseil du Seigneur, et de ceux qui tremblent au commandement de notre Dieu; et qu'il en soit fait selon la Loi.
Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
4 Lève-toi, car cette affaire te regarde, et nous serons avec toi; prends donc courage, et agis.
Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
5 Alors Esdras se leva, et fit jurer les principaux des Sacrificateurs, des Lévites, et de tout Israël, qu'ils feraient selon cette parole; et ils jurèrent.
Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
6 Puis Esdras se leva de devant la maison de Dieu, et s'en alla dans la chambre de Johanan fils d'Eliasib, et y entra; et il ne mangea point de pain, ni ne but point d'eau, parce qu'il menait deuil à cause du péché de ceux de la captivité.
Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
7 Alors on publia dans le pays de Juda et dans Jérusalem, à tous ceux qui étaient retournés de la captivité, qu'ils eussent à s'assembler à Jérusalem.
Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
8 Et que quiconque ne s'y rendrait pas dans trois jours, selon l'avis des principaux et des Anciens, tout son bien serait mis à l'interdit, et que pour lui, il serait séparé de l'assemblée de ceux de la captivité.
Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
9 Ainsi tous ceux de Juda et de Benjamin s'assemblèrent à Jérusalem dans les trois jours, ce qui fut au neuvième mois le vingtième jour du mois; et tout le peuple se tint devant la place de la maison de Dieu, tremblant pour ce sujet, et à cause des pluies.
A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
10 Puis Esdras le Sacrificateur se leva, et leur dit: Vous avez péché en ce que vous avez pris chez vous des femmes étrangères, de sorte que vous avez augmenté le crime d'Israël.
Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
11 Mais maintenant faites confession [de votre faute] à l'Eternel le Dieu de vos pères, et faites sa volonté, et séparez-vous des peuples du pays, et des femmes étrangères.
Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
12 Et toute l'assemblée répondit, et dit à haute voix: C'est notre devoir de faire ce que tu as dit;
Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
13 Mais le peuple est grand, et ce temps est fort pluvieux, c'est pourquoi il n'[y a] pas moyen de demeurer dehors, et cette affaire n'est pas d'un jour, ni de deux; car nous sommes beaucoup de gens qui avons péché en cela.
Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
14 Que tous les principaux d'entre nous comparaissent donc devant toute l'assemblée, et que tous ceux qui sont dans nos villes, et qui ont pris chez eux des femmes étrangères, viennent en certain temps, et que les Anciens de chaque ville et ses juges soient avec eux; jusqu'à ce que nous détournions de nous l'ardeur de la colère de notre Dieu, [et] que ceci soit achevé.
Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
15 Et Jonathan fils d'Hazaël, et Jahzéja fils de Tikva furent établis pour cette affaire; et Mésullam et Sabéthaï, Lévites, les aidèrent.
Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
16 Et ceux qui étaient retournés de la captivité en firent de même, tellement qu'on choisit Esdras le Sacrificateur, [et] ceux qui étaient les Chefs des pères selon les maisons de leurs pères, tous [nommés] par leurs noms, qui commencèrent leurs séances le premier jour du dixième mois, pour s'informer du fait.
Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
17 Et le premier jour du premier mois ils eurent fini avec tous ceux qui avaient pris chez eux des femmes étrangères.
A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
18 Or quant aux fils des Sacrificateurs qui avaient pris chez eux des femmes étrangères, il se trouva d'entre les enfants de Jésuah, fils de Jotsadak et de ses frères, Mahaséja, Elihézer, Jarib, et Guédalia;
A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
19 Qui donnèrent les mains à renvoyer leurs femmes; et avouant qu'ils étaient coupables, [ils offrirent] pour leur délit un bélier du troupeau.
(Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
20 Des enfants d'Immer, Hanani, et Zébadia;
Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
21 Et des enfants de Harim, Mahaséja, Elie, Sémahia, Jéhiël, et Huzija;
Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
22 Et des enfants de Pashur, Eliohenaï, Mahaséja, Ismaël, Nathanaël, Jozabad, et Elhasa;
Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
23 Et des Lévites, Jozabad, Simhi, Kélaja, (qui est le même que Kélita) Péthahia, Juda, et Elihézer;
Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
24 Et des chantres, Eliasib; et des portiers, Sallum, Telem, et Uri.
Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
25 Et de ceux d'Israël; des enfants de Parhos, Ramia, Jizija, Malkija, Mijamin, Elhazar, Malkija et Bénaja;
Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
26 Et des enfants de Hélam, Mattania, Zacharie, Jéhiël, Habdi, Jérémoth, et Elie;
Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
27 Et des enfants de Zattu, Eliohénaï, Eliasib, Mattania, Jérémoth, Zabad, et Haziza;
Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
28 Et des enfants de Bébaï, Johanan, Hanania, Zabbaï, et Hathlaï;
Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
29 Et des enfants de Bani, Mésullam, Malluc, Hadaja, Jasub, Séal, et Ramoth;
Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
30 Et des enfants de Pahath-Moab, Hadna, Kélal, Bénaja, Mahaséja, Mattania, Bethsaléël, Binnuï, et Manassé;
Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
31 Et des enfants de Harim, Elihézer, Jisija, Malkija, Sémahia, Siméon;
Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
32 Benjamin, Malluc [et] Semaria;
Benyamin, Malluk da Shemariya.
33 [Et] des enfants de Masum, Mattenaï, Mattata, Zabad, Eliphélet, Jérémaï, Manassé, et Simhi;
Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
34 [Et] des enfants de Bani, Mahadaï, Hamram, Uël,
Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
35 Bénaja, Bédéja, Kéluhu,
Benahiya, Bedeya, Keluhi,
36 Vania, Mérémoth, Eliasib,
Baniya, Meremot, Eliyashib,
37 Mattania, Matténaï, Jahasaï,
Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
38 Bani, Binnuï, Simhi,
Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
39 Sélémia, Nathan, Hadaja,
Shelemiya, Natan, Adahiya,
40 Mabnadbaï, Sasaï, Saraï,
Maknadebai, Shashai, Sharai,
41 Hazaréel, Sélémia, Sémaria,
Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
42 Sallum, Amaria, et Joseph;
Shallum da Amariya da Yusuf.
43 [Et] des enfants de Nébo, Jéhiël, Mattitia, Zabad, Zébina, Jaddan, Joël, et Bénaja.
Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
44 Tous ceux-là avaient pris des femmes étrangères; et il y avait quelques-uns d'entr'eux qui avaient eu des enfants de ces femmes-là.
Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.

< Esdras 10 >