< Ézéchiel 30 >

1 La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d'homme, prophétise, et dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: hurlez, [et dites]: ah quelle journée!
“Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
3 Car la journée [est] proche, oui la journée de l'Eternel est proche, c'est une journée de nuage; ce sera le temps des nations.
Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
4 L'épée viendra sur l'Egypte, et il y aura de l'effroi en Cus, quand ceux qui seront blessés à mort tomberont dans l'Egypte, et quand on enlèvera la multitude de son peuple, et que ses fondements seront ruinés.
Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
5 Cus, et Put, et Lud, et tout le mélange [d'Arabie], et Cub, et les enfants du pays allié tomberont par l'épée avec eux.
Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
6 Ainsi a dit l'Eternel: ceux qui soutiendront l'Egypte, tomberont; et l'orgueil de sa force sera renversé; ils tomberont en elle par l'épée depuis la tour de Syène, dit le Seigneur l'Eternel.
“‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
7 Et ils seront désolés au milieu des pays désolés, et ses villes seront au milieu des villes rendues désertes.
Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
8 Et ils sauront que je suis l'Eternel, quand j'aurai mis le feu en Egypte; et tous ceux qui lui donneront du secours, seront brisés.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
9 En ce jour-là des messagers sortiront de ma part dans des navires pour effrayer Cus l'assurée, et il y aura entre eux un tourment tel qu'à la journée d'Egypte; car voici, il vient.
“‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
10 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je ferai périr la multitude d'Egypte par la puissance de Nébucadnetsar, Roi de Babylone.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
11 Lui et son peuple avec lui, les plus terribles d'entre les nations, seront amenés pour ruiner le pays, et ils tireront leurs épées contre les Egyptiens, et rempliront la terre de morts.
Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
12 Et je mettrai à sec les bras [d'eau], et je livrerai le pays entre les mains de gens méchants, je désolerai le pays, et tout ce qui y est, par la puissance des étrangers; moi l'Eternel j'ai parlé.
Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
13 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je détruirai aussi les idoles, j'anéantirai les faux dieux de Noph, et il n'y aura point de Prince qui soit du pays d'Egypte; et je mettrai la frayeur dans le pays d'Egypte.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
14 Je désolerai Pathros, je mettrai le feu à Tsohan, et j'exercerai des jugements dans No.
Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
15 Et je répandrai ma fureur sur Sin, qui est la force d'Egypte, et j'exterminerai la multitude qui est à No.
Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
16 Quand je mettrai le feu en Egypte, Sin sera grièvement tourmentée, et No sera rompue par diverses brèches, et il n'y aura à Noph que détresses en plein jour.
Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
17 Les jeunes gens d'élite d'Aven et de Pibeseth tomberont par l'épée, et elles iront en captivité.
Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
18 Et le jour défaudra dans Taphnès, lorsque j'y romprai les barres d'Egypte, et que l'orgueil de sa force aura cessé; une nuée la couvrira, et les villes de son ressort iront en captivité.
Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
19 Et j'exercerai des jugements en Egypte; et ils sauront que je suis l'Eternel.
Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
20 Or il était arrivé en la onzième année, au septième jour du premier mois, que la parole de l'Eternel m'avait été adressée, en disant:
A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
21 Fils d'homme, j'ai rompu le bras de Pharaon Roi d'Egypte; et voici on ne l'a point bandé pour le guérir, en sorte qu'on lui ait mis des linges pour le bander, [et] pour le fortifier, afin qu'il pût empoigner l'épée.
“Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
22 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici, j'en veux à Pharaon Roi d'Egypte, et je romprai ses bras, tant celui qui est fort, que celui qui est rompu, et je ferai tomber l'épée de sa main.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
23 Et je disperserai les Egyptiens parmi les nations, et les répandrai parmi les pays.
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
24 Et je fortifierai les bras du Roi de Babylone, et je lui mettrai mon épée en la main; mais je romprai les bras de Pharaon, et [Pharaon] jettera des sanglots devant lui, comme des gens blessés à mort.
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
25 Je fortifierai donc les bras du Roi de Babylone, mais les bras de Pharaon tomberont; et on saura que je suis l'Eternel, quand j'aurai mis mon épée en la main du Roi de Babylone, et qu'il l'aura étendue sur le pays d'Egypte.
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
26 Et je disperserai les Egyptiens parmi les nations, et les répandrai parmi les pays; et ils sauront que je suis l'Eternel.
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ézéchiel 30 >