< Ézéchiel 17 >
1 Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d'homme, propose une énigme, et mets en avant une similitude à la maison d'Israël.
“Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
3 Et dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: une grand aigle à grandes ailes, et d'un long plumage, pleine de plumes comme en façon de broderie, est venue au Liban, et a enlevé la cime d'un cèdre;
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
4 Elle a rompu le bout de ses jets, et l'a transporté en un pays marchand, et l'a mis dans une ville de négociants.
ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
5 Et elle a pris de la semence du pays, et l'a mise en un champ propre à semer, [et] la portant près des grosses eaux, l'a plantée [comme] un saule.
“‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
6 Cette [semence] poussa, et devint un cep vigoureux, [mais] bas, ayant ses rameaux tournés vers cette [aigle], et ses racines étant sous elle; cette [semence] devint donc un cep, et produisit des sarments et poussa des rejetons.
ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
7 Mais il y avait une [autre] grande aigle à grandes ailes, et de beaucoup de plumes; et voici ce cep serra vers elle ses racines, et étendit ses branches vers elle, afin qu'elle l'arrosât [des eaux qui coulaient dans les] carreaux de son parterre.
“‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
8 Il était donc planté en une bonne terre, près des grosses eaux, en sorte qu'il jetait des sarments et portait du fruit, et il était devenu un cep excellent.
An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
9 Dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel, viendra-t-il à bien? n'arrachera-t-elle pas ses racines, et ne coupera-t-elle pas ses fruits, et ils deviendront secs? tous les sarments qu'il a jetés sécheront, et il ne faudra pas même un grand effort, et beaucoup de monde, pour l'enlever de dessus ses racines.
“Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
10 Mais voici, [quoique] planté, viendra-t-il pourtant à bien? Quand le vent d'Orient l'aura touché, ne séchera-t-il pas entièrement? il séchera sur le terrain où il était planté.
Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
11 Puis la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 Dis maintenant à la maison rebelle: ne savez-vous pas ce que veulent dire ces choses? Dis: voici, le Roi de Babylone est venu à Jérusalem, et en a pris le Roi, et les Princes, et les a emmenés avec lui à Babylone.
“Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
13 Et il en a pris un de la race Royale, il a traité alliance avec lui, il lui a fait prêter serment avec exécration, et il a retenu les puissants du pays.
Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
14 Afin que le Royaume fût tenu bas, et qu'il ne s'élevât point, [mais] qu'en gardant son alliance, il subsistât.
don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
15 Mais celui-ci s'est rebellé contre lui, envoyant ses messagers en Egypte, afin qu'on lui donnât des chevaux, et un grand peuple. Celui qui fait de telles choses prospérera-t-il? échappera-t-il? et ayant enfreint l'alliance, échappera-t-il?
Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
16 Je suis vivant, dit le Seigneur l'Eternel, si celui-ci ne meurt au pays du Roi qui l'a établi pour Roi, parce qu'il a méprisé le serment d'exécration qu'il lui avait fait, et parce qu'il a enfreint l'alliance qu'il avait faite avec lui, si, [dis-je, il ne meurt dans] Babylone.
“‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
17 Et Pharaon ne fera rien pour lui dans la guerre, avec une grande armée et beaucoup de troupes, lorsque [l'ennemi] aura dressé des terrasses, et bâti des bastions pour exterminer beaucoup de gens.
Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
18 Parce qu'il a méprisé le serment d'exécration en violant l'alliance; car voici, après avoir donné sa main, il a fait néanmoins toutes ces choses-là; il n'échappera point.
Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
19 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je suis vivant, si je ne fais tomber sur sa tête mon serment d'exécration qu'il a méprisé, et mon alliance qu'il a enfreinte.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
20 Et j'étendrai mon rets sur lui, et il sera pris dans mes filets, et je le ferai entrer dans Babylone, et là j'entrerai en jugement contre lui pour le crime qu'il a commis contre moi.
Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
21 Et tous ses fugitifs avec toutes ses troupes tomberont par l'épée, et ceux qui demeureront de reste seront dispersés à tout vent; et vous saurez que moi l'Eternel j'ai parlé.
Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
22 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je prendrai aussi [un rameau] de la cime de ce haut cèdre, et je le planterai; je couperai, dis-je, du bout de ses jeunes branches un tendre rameau, et je le planterai sur une montagne haute et éminente.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
23 Je le planterai sur la haute montagne d'Israël, et là il produira des branches, et fera du fruit, et il deviendra un excellent cèdre; et des oiseaux de tout plumage demeureront sous lui, [et] habiteront sous l'ombre de ses branches.
A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
24 Et tous les bois des champs connaîtront que moi l'Eternel j'aurai abaissé le grand arbre, et élevé le petit arbre, fait sécher le bois vert, et fait reverdir le bois sec; moi l'Eternel, j'ai parlé, et je le ferai.
Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”