< Ézéchiel 10 >

1 Puis je regardai, et voici dans l'étendue qui était sur la tête des Chérubins parut au-dessus d'eux comme une pierre de saphir, qui, à la voir, était semblable à un trône.
Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
2 Et on parla à l'homme vêtu de lin, et on lui dit: entre dans l'entre-deux des roues au dessous du Chérubin, et remplis tes paumes de charbons de feu de l'entre-deux des Chérubins, et les répands sur la ville; il y entra donc, moi le voyant.
Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
3 Et les Chérubins se tenaient à main droite de la maison quand l'homme entra; et une nuée remplit le parvis intérieur.
Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
4 Puis la gloire de l'Eternel s'éleva de dessus les Chérubins pour venir sur le seuil de la maison, et la maison fut remplie d'une nuée; le parvis aussi fut rempli de la splendeur de la gloire de l'Eternel.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
5 Et on entendit le bruit des ailes des Chérubins jusqu'au parvis extérieur, comme la voix du [Dieu] Fort Tout-puissant, quand il parle.
Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
6 Et il arriva que quand il eut commandé à l'homme qui était vêtu de lin, en disant: prends du feu de l'entre-deux des Chérubins; il entra, et se tint auprès des roues.
Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
7 Et l'un des Chérubins étendit sa main vers l'entre-deux des Chérubins au feu qui était dans l'entre-deux des Chérubins; et il en prit, et le mit entre les mains de l'homme vêtu de lin, qui l'ayant reçu, se retira.
Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
8 (Car il apparaissait dans les Chérubins la figure d'une main d'homme sous leurs ailes.)
(A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
9 Puis je regardai, et voici quatre roues auprès des Chérubins, une roue auprès d'un des Chérubins, et une autre roue auprès d'un Chérubin; et la ressemblance des roues était comme la couleur d'une pierre de chrysolithe.
Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
10 Et quant à leur ressemblance, toutes quatre avaient une même façon, comme si une roue eût été au dedans d'une autre roue.
Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
11 Quand elles marchaient, elles allaient sur leurs quatre côtés; et en marchant elles ne se tournaient point, mais au lieu vers lequel le chef tendait, elles allaient après lui; elles ne se tournaient point quand elles marchaient.
Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
12 Non plus que tout le corps des Chérubins, ni leur dos, ni leurs mains, ni leurs ailes; et les roues, [savoir] leurs quatre roues, étaient pleines d'yeux à l'entour.
Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
13 Et quant aux roues, on les appela, moi l'entendant, un chariot.
Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
14 Et chaque [animal] avait quatre faces: la première face était la face d'un Chérubin; et la seconde face [était] la face d'un homme; et la troisième [était] la face d'un lion; et la quatrième la face d'un aigle.
Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
15 Puis les Chérubins s'élevèrent en haut. Ce sont là les animaux que j'avais vus auprès du fleuve de Kébar.
Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
16 Et lorsque les Chérubins marchaient, les roues aussi marchaient auprès d'eux, et quand les Chérubins élevaient leurs ailes pour s'élever de terre, les roues ne se contournaient point d'auprès d'eux.
Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
17 Lorsqu'ils s'arrêtaient, elles s'arrêtaient; et lorsqu'ils s'élevaient, elles s'élevaient; car l'esprit des animaux [était] dans les roues.
Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
18 Puis la gloire de l'Eternel se retira de dessus le seuil de la maison, et se tint au dessus des Chérubins.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
19 Et les Chérubins élevant leurs ailes, s'élevèrent de terre en ma présence quand ils partirent; et les roues [s'élevèrent] aussi vis-à-vis d'eux, et chacun d'eux s'arrêta à l'entrée de la porte Orientale de la maison de l'Eternel; et la gloire du Dieu d'Israël était sur eux par dessus.
Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
20 Ce sont là les animaux que j'avais vus sous le Dieu d'Israël près du fleuve de Kébar; et je connus que c'étaient des Chérubins.
Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
21 Chacun avait quatre faces, et chacun quatre ailes, et il y avait une ressemblance de main d'homme sous leurs ailes.
Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
22 Et quant à la ressemblance de leurs faces, c'étaient les faces que j'avais vues auprès du fleuve de Kébar, et leur [même] regard, et elles-mêmes; et chacun marchait vis-à-vis de soi.
Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.

< Ézéchiel 10 >