< Esther 5 >

1 Et il arriva qu'au troisième jour Esther se vêtit d'un habit Royal, et se tint au parvis de dedans du palais du Roi [qui était] au devant de l'hôtel du Roi, et le Roi était assis sur le trône de son Royaume dans le palais Royal, vis-à-vis de la porte du palais.
A rana ta uku, Esta ta sanya rigunanta na sarauta, ta tafi ta tsaya a harabar fada, a gaban zaure sarki. Sarki yana zaune a kan gadon sarautarsa a zauren, yana fuskantar ƙofar shiga.
2 Or dès que le Roi vit la Reine Esther qui se tenait debout au parvis, elle gagna ses bonnes grâces; de sorte que le Roi tendit à Esther le sceptre d'or qui était en sa main; et Esther s'approcha, et toucha le bout du sceptre.
Sa’ad da ya ga Sarauniya Esta tsaye a harabar, sai ya ji daɗin ganinta, ya miƙa mata sandan sarauta na zinariya da take hannunsa. Sai Esta ta matsa kusa ta taɓa kan sandan.
3 Et le Roi lui dit: Qu'as-tu Reine Esther? et quelle est ta demande? quand ce serait jusqu'à la moitié du Royaume, il te sera donné.
Sai sarki ya ce mata, “Me kike so, Sarauniya Esta? Mene ne roƙonki? Kai, ko rabin masarautata ce, za a ba ki.”
4 Et Esther répondit: Si le Roi le trouve bon, que le Roi vienne aujourd'hui avec Haman au festin que je lui ai préparé.
Esta ta ce, “In ya gamshi sarki, bari sarki, tare da Haman su zo wurin liyafar da na shirya wa sarki yau.”
5 Alors le Roi dit: Qu'on fasse venir en diligence Haman, pour accomplir la parole d'Esther. Le Roi donc vint avec Haman au festin qu'Esther avait préparé.
Sai sarki ya ce, “Maza a kawo Haman don mu yi abin da Esta ta roƙa.” Saboda haka, sarki da Haman suka tafi liyafar da Esta ta shirya.
6 Et le Roi dit à Esther au vin de la collation: Quelle est ta demande? et elle te sera octroyée. Et quelle est ta prière? [quand tu me demanderais] jusqu'à la moitié du Royaume, cela sera fait.
Yayinda suke shan ruwan inabi, sarki ya sāke ce wa Esta, “Yanzu, mece ce bukatarki? Za a biya miki shi. Kuma mene ne roƙonki? Kai, ko rabin masarautata ce, za a ba ki.”
7 Alors Esther répondit, et dit: Ma demande, et ma prière est,
Esta ta amsa ta ce, “Bukatata da kuma roƙona shi ne,
8 Si j'ai trouvé grâce devant le Roi, et si le Roi trouve bon d'accorder ma demande, et d'exaucer ma requête; que le Roi et Haman viennent au festin que je leur préparerai, et je ferai demain selon la parole du Roi.
in na sami tagomashi a wurin sarki, in kuma sarki ya yarda yă biya mini bukatata, yă kuma ji roƙona, bari sarki da Haman su zo gobe wurin liyafar da zan shirya musu. Sa’an nan zan amsa tambayar sarki.”
9 Et Haman sortit en ce jour-là, joyeux et le cœur gai. Mais sitôt qu'il eut vu à la porte du Roi Mardochée, qui ne se leva point, et ne se remua point pour lui, Haman fut rempli de colère contre Mardochée.
Haman ya fita a ranan da murna, ya kuma ji daɗi. Amma sa’ad da ya ga Mordekai a bakin ƙofar sarki, ya kuma lura cewa bai tashi, ko yă nuna bangirma a gabansa ba, sai ya cika da fushi.
10 Toutefois Haman se fit violence, et vint en sa maison; puis il envoya quérir ses amis, et Zérès sa femme.
Duk da haka, Haman ya cije, ya tafi gida. Sai ya kira abokansa da kuma matarsa, Zeresh,
11 Alors Haman leur raconta la gloire de ses richesses, et l'excellence de ses enfants, et toutes les choses dans lesquelles le Roi l'avait agrandi, et comment il l'avait élevé par-dessus les principaux Seigneurs et Serviteurs du Roi.
ya yi ta taƙama game da ɗumbun wadatarsa, da yawan’ya’yansa maza, da dukan yadda sarki ya girmama shi, ya kuma ɗaga shi bisan sauran hakimai da shugabanni.
12 Puis Haman dit: Et même la Reine Esther n'a fait venir que moi avec le Roi au festin qu'elle a fait, et je suis encore demain convié par elle avec le Roi.
Haman ya ƙara da cewa, “Ba duka ke nan ba, kai, ni ne kaɗai mutumin da Sarauniya Esta ta gayyata yă tafi tare da sarki zuwa liyafar da ta shirya. Ta sāke gayyace ni tare da sarki gobe.
13 Mais tout cela ne me sert de rien, pendant tout le temps que je vois Mardochée, ce Juif, séant à la porte du Roi.
Amma dukan wannan bai biya mini bukata ba, muddin ina ganin wannan mutumin Yahudan nan Mordekai, yana zama a bakin ƙofar sarki.”
14 Alors Zérès sa femme, et tous ses amis lui répondirent: Qu'on fasse un gibet haut de cinquante coudées, et demain au matin dis au Roi qu'on y pende Mardochée; et va-t'en joyeux au festin avec le Roi. Et la chose plut à Haman, et il fit faire le gibet.
Matarsa Zeresh, da dukan abokansa suka ce masa, “Ka sa a gina wurin rataye mai laifi, mai tsawo, ƙafa saba’in da biyar, da safe kuwa ka ce wa sarki a rataye Mordekai a kansa. Sa’an nan ka tafi cin abincin dare tare da sarki da murna.” Wannan shawarar ta faranta wa Haman rai, ya kuma sa aka gina wurin rataye mai laifi.

< Esther 5 >