< Deutéronome 4 >

1 Et maintenant Israël, écoute ces statuts et ces droits que je t'enseigne, pour [les] faire afin que vous viviez, et que vous entriez au pays que l'Eternel le Dieu de vos pères vous donne, et que vous le possédiez.
To, ku ji, ya Isra’ila, ku kasa kunne ga ƙa’idodi da dokokin da nake shirin koya muku. Ku bi su domin ku yi tsawon rai, ku kuma shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku yake ba ku.
2 Vous n'ajouterez rien à la parole que je vous commande, et vous n'en diminuerez rien, afin de garder les commandements de l'Eternel votre Dieu lesquels je vous commande [de garder].
Kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin abin da nake umarce ku. Amma ku kiyaye umarnan nan na Ubangiji Allahnku, da na ba ku.
3 Vos yeux ont vu ce que l'Eternel a fait à cause de Bahal-Péhor; car l'Eternel ton Dieu a détruit du milieu de toi tout homme qui était allé après Bahal-Péhor.
Da idanunku, kun ga abin da Ubangiji ya yi a Ba’al-Feyor. Yadda Ubangiji Allahnku ya hallaka waɗansu daga cikinku waɗanda suka yi wa Ba’al-Feyor sujada,
4 Mais vous qui vous êtes attachés à l'Eternel votre Dieu, vous êtes tous vivants aujourd'hui.
Amma ku da kuka manne ga Ubangiji Allahnku, kuna da rai har wa yau.
5 Regardez, je vous ai enseigné les statuts et les droits, comme l'Eternel mon Dieu me l'a commandé, afin que vous fassiez ainsi au milieu du pays dans lequel vous allez entrer pour le posséder.
Ga shi, na koya muku ƙa’idodi da dokoki, yadda Ubangiji Allahna ya umarce ni, don ku bi su a ƙasar da za ku shiga ku mallaki.
6 Vous les garderez donc et les ferez; car c'est là votre sagesse et votre intelligence devant tous les peuples, qui entendant ces statuts, diront: Cette grande nation est le seul peuple sage et intelligent.
Ku kiyaye su, ku aikata su, gama yin haka zai tabbatar wa sauran al’ummai, kuna da hikima da ganewa. Sa’ad da al’ummai za su ji waɗannan dokoki, za su ce, “Ba shakka, wannan babbar al’umma tana da hikima da ganewa.”
7 Car quelle [est] la nation si grande, qui ait ses dieux près de soi, comme nous avons l'Eternel notre Dieu en tout ce pour quoi nous l'invoquons?
Wace al’umma ce mai girma haka wadda allolinta take kusa da su yadda Ubangiji Allahnmu yake kusa da mu a duk sa’ad da muka yi addu’a gare shi?
8 Et quelle est la nation si grande, qui ait des statuts et des ordonnances justes, comme est toute cette Loi que je mets aujourd'hui devant vous?
Wace al’umma ce mai girma haka wadda take da ƙa’idodi da dokoki masu adalci kamar waɗannan ƙunshin dokokin da nake sa a gabanku a yau?
9 Seulement prends garde à toi, et garde soigneusement ton âme, afin que tu n'oublies point les choses que tes yeux ont vues, et afin que de tous les jours de ta vie elles ne sortent de ton cœur, mais que tu les enseignes à tes enfants, et aux enfants de tes enfants.
Ku kula, ku kuma lura da kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da idanunku suka gani, ko kuwa ku bari su fita daga zuciyarku muddin ranku. Ku koyar da su ga’ya’yanku, da’ya’yan’ya’yanku.
10 Le jour que tu te tins devant l'Eternel ton Dieu en Horeb, après que l'Eternel m'eut dit: Assemble le peuple, afin que je leur fasse entendre mes paroles, lesquelles ils apprendront pour me craindre tout le temps qu'ils seront vivants sur la terre, et pour [les] enseigner à leurs enfants;
Ku tuna da ranar da kuka tsaya a gaban Ubangiji Allahnku a Horeb, sa’ad da ya ce mini, “Ka tara mutane a gabana, don su ji maganata, su koya yin mini bangirma muddin ransu a ƙasar, su kuma iya koyar da su ga’ya’yansu.”
11 Et que vous vous approchâtes, et vous tîntes sous la montagne. Or la montagne était toute en feu jusqu'au milieu du ciel, et il y avait des ténèbres, une nuée, et une obscurité.
Sai kuka matso kusa, kuka tsaya a gindin dutse yayinda yana cin wuta har zuwa sararin sama, ga kuma baƙin gizagizai da kuma baƙin duhu.
12 Et que l'Eternel vous parla du milieu du feu; vous entendiez bien une voix qui parlait, mais vous ne voyiez aucune ressemblance, [vous entendiez] seulement la voix.
Sai Ubangiji ya yi magana daga wutar. Kuka ji furcin kalmomin, amma ba ku ga siffar kome ba, sai dai murya kaɗai kuka ji.
13 Et il vous fit entendre son alliance, laquelle il vous commanda d'observer, [savoir] les dix paroles qu'il écrivit dans deux Tables de pierre.
Ya furta alkawarinsa gare ku, Dokoki Goma, waɗanda ya umarce ku ku bi, ya kuma rubuta su a alluna biyu.
14 L'Eternel me commanda aussi en ce temps-là de vous enseigner les statuts et les droits, afin que vous les fassiez au pays dans lequel vous allez passer pour le posséder.
Sa’an nan Ubangiji ya umarce ni a wannan lokaci, in koya muku ƙa’idodi da dokokin da za ku bi a ƙasar da kuke hayewa Urdun don mallake.
15 Vous prendrez donc bien garde à vos âmes, car vous n'avez vu aucune ressemblance au jour que l'Eternel votre Dieu vous parla en Horeb du milieu du feu;
Ba ku ga wata siffa a ranar da Ubangiji ya yi magana da ku a Horeb daga wuta ba. Saboda haka ku lura da kanku sosai,
16 De peur que vous ne vous corrompiez, et que vous ne vous fassiez quelque image taillée, ou quelque représentation ayant la forme d'un mâle ou d'une femelle;
don kada ku lalace, ku kuma yi wa kanku gunki, siffa ta wani kama, ko a kamannin namiji, ko kuwa ta mace,
17 Ou l'effigie d'aucune bête qui soit en la terre, ou l'effigie d'aucun oiseau ayant des ailes, qui vole par les cieux;
ko a kamannin wata dabba a duniya, ko na wani tsuntsun da yake tashi a sama,
18 Ou l'effigie d'aucun reptile qui rampe sur la terre; ou l'effigie d'aucun poisson qui soit dans les eaux au dessous de la terre.
ko kuwa a kamannin wata halittar da take rarrafe a ƙasa, ko na wani kifi a cikin ruwaye a ƙarƙashi.
19 De peur aussi qu'élevant tes yeux vers les cieux, et qu'ayant vu le soleil, la lune, et les étoiles, toute l'armée des cieux, tu ne sois poussé à te prosterner devant elles, et que tu ne les serves; vu que l'Eternel ton Dieu les a donnés en partage à tous les peuples qui sont sous tous les cieux.
Sa’ad da kuka ɗaga ido kuka kali sama, kuka ga rana da wata, da taurari, da dukan halittun sama, sai ku kula fa, kada ku jarrabtu, ku ce za ku yi musu sujada, ko ku bauta musu; abubuwan nan Ubangiji Allahnku ne ya rarraba wa dukan al’umman da suke ko’ina a ƙarƙashin sararin sama.
20 Et l'Eternel vous a pris, et vous a tirés hors d'Egypte, hors du fourneau de fer; afin que vous lui soyez un peuple héréditaire, comme il paraît aujourd'hui.
Amma ku, Ubangiji ya ɗauke ku, ya fid da ku daga matuya mai narken ƙarfe, wato, daga Masar, domin ku zama jama’arsa ta musamman kamar yadda kuke a yau.
21 Or l'Eternel a été irrité contre moi, à cause de vos paroles, et il a juré que je ne passerais point le Jourdain, et que je n'entrerais point en ce bon pays que l'Eternel ton Dieu te donne en héritage.
Ubangiji ya yi fushi da ni saboda ku, ya kuma yi rantsuwa cewa ba zan haye Urdun, in shiga ƙasan nan mai kyau da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo ba.
22 Et de fait je m'en vais mourir en ce pays-ci sans que je passe le Jourdain; mais vous l'allez passer, et vous posséderez ce bon pays-là.
Zan mutu a wannan ƙasa; ba zan haye Urdun ba; amma kuna gab da ƙetarewa, ku mallaki wannan ƙasa mai kyau.
23 Donnez-vous de garde que vous n'oubliiez l'alliance de l'Eternel votre Dieu, laquelle il a traitée avec vous, et que vous ne vous fassiez quelque image taillée, ou la ressemblance de quelque chose que ce soit, selon que l'Eternel votre Dieu vous l'a défendu.
Ku yi hankali kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku; kada fa ku yi wa kanku gunki a kamannin wani abin da Ubangiji Allahnku ya hana.
24 Car l'Eternel ton Dieu est un feu consumant; c'est le [Dieu] Fort, qui est jaloux.
Gama Ubangiji Allahnku wuta ne mai ƙuna, Allah ne mai kishi.
25 Quand tu auras engendré des enfants, et que tu auras eu des enfants de tes enfants, et que tu seras habitué dès longtemps au pays, si alors vous vous corrompez, et que vous fassiez quelque image taillée, ou la ressemblance de quelque chose que ce soit, et si vous faites ce qui déplaît à l'Eternel votre Dieu, afin de l'irriter;
Bayan kun haifi’ya’ya da jikoki, kuka kuma zauna na dogon lokaci a ƙasar, in har kuka lalace, kuka kuma yi wani irin gunki, kuna aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnku, kuna kuma sa shi fushi.
26 J'appelle aujourd'hui à témoin les cieux et la terre contre vous, que certainement vous périrez aussitôt dans ce pays pour lequel posséder vous allez passer le Jourdain, [et] vous n'y prolongerez point vos jours; mais vous serez entièrement détruits.
Yau, na kira sama da duniya, su zama shaidata a kanku. Idan kuka yi rashin biyayya, lalle za ku hallaka nan da nan daga ƙasar da kuke ƙetare Urdun ku gāda. Ba za ku daɗe a cikinta ba, amma za a kawar da ku ƙaƙaf.
27 Et l'Eternel vous dispersera entre les peuples, et il ne restera de vous qu'un petit nombre parmi les nations, chez lesquelles l'Eternel vous fera emmener.
Ubangiji zai watsar da ku a cikin mutane, ɗan kaɗan ne kaɗai za su ragu a cikin al’umman da Ubangiji zai kai ku.
28 Et vous serez là asservis à des dieux qui sont des œuvres de main d'homme, du bois, et de la pierre, qui ne voient ni n'entendent, qui ne mangent point, et ne flairent point.
A can za ku bauta wa allolin da mutum ya yi, na itace da dutse da ba sa gani, ba sa ji, ba sa ci, ba kuma iya sansanawa.
29 Mais tu chercheras de là l'Eternel ton Dieu; et tu [le] trouveras, parce que tu l'auras cherché de tout ton cœur, et de toute ton âme.
Amma daga can in kuka nemi Ubangiji Allahnku, da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, za ku same shi.
30 Quand tu seras dans l'angoisse, et que toutes ces choses te seront arrivées, alors, au dernier temps, tu retourneras à l'Eternel ton Dieu, et tu obéiras à sa voix.
Sa’ad da kuke cikin wahala saboda waɗannan abubuwan da suka same ku nan gaba, to, sai ku juyo ga Ubangiji Allahnku, ku kuma yi masa biyayya.
31 Parce que l'Eternel ton Dieu est le [Dieu] Fort, [et] miséricordieux, il ne t'abandonnera point, il ne te détruira point, et il n'oubliera point l'alliance de tes pères qu'il leur a jurée.
Gama Ubangiji Allahnku, Allah ne mai jinƙai; ba zai yashe ku ko yă hallaka, ko kuma yă manta da alkawarin da ya yi da kakanninku, wanda ya tabbatar da su da rantsuwa ba.
32 Car informe-toi des premiers temps, qui ont été avant toi, depuis le jour que Dieu a créé l'homme sur la terre, et depuis un bout des cieux jusqu'à l'autre bout, s'il a jamais été rien fait de semblable à cette grande chose, et s'il a été [jamais] rien entendu de semblable.
Ku bincika dukan tarihi mana, tun daga lokacin da Allah ya halicci mutane a cikin duniya har yă zuwa yanzu; ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?
33 [Savoir], qu'un peuple ait entendu la voix de Dieu parlant du milieu du feu, comme tu l'as entendue, et qu'il soit demeuré en vie.
Akwai waɗansu mutanen da suka taɓa jin muryar Allah yana magana daga wuta, kamar yadda kuka ji har suka rayu?
34 Ou que Dieu ait fait une telle épreuve, que de venir prendre à soi une nation du milieu d'une [autre] nation, par des épreuves, des signes et des miracles, par des batailles, et à main forte, et à bras étendu, et par des choses grandes et terribles, selon tout ce que l'Eternel notre Dieu a fait pour vous en Egypte, vous le voyant.
Akwai wani allahn da ya taɓa yin ƙoƙari yă ɗauko wa kansa wata al’umma daga wata al’umma, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu masu banmamaki da al’ajabai, ta wurin yaƙi, ta wurin hannu mai iko, da kuma hannu mai ƙarfi, ko kuwa ta wurin ayyuka masu bangirma da na banmamaki, kamar dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi saboda ku a Masar, a kan idanunku?
35 Ce qui t'a été montré, afin que tu connusses que l'Eternel est celui qui est Dieu, [et] qu'il n'y en a point d'autre que lui.
An nuna muku dukan waɗannan abubuwa saboda ku san cewa Ubangiji, shi ne Allah; ban da shi, babu wani.
36 Il t'a fait entendre sa voix des cieux pour t'instruire, et il t'a montré son grand feu en la terre, et tu as entendu ses paroles du milieu du feu.
Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, don yă hore ku. A duniya ya nuna muku wutarsa mai girma, kuka kuma ji kalmominsa daga wuta.
37 Et parce qu'il a aimé tes pères il a choisi leur postérité après eux, et t'a retiré d'Egypte devant sa face, par sa grande puissance.
Domin ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓi zuriyarsu a bayansu, ya fitar da ku daga Masar ta wurin kasancewarsa da kuma ƙarfinsa mai girma,
38 Pour chasser de devant toi des nations plus grandes et plus robustes que toi, pour t'introduire en leur pays, et pour te le donner en héritage, comme il paraît aujourd'hui.
don yă fitar da ku a gaban al’ummai da suka fi ku girma da kuma ƙarfi, ya kawo ku cikin ƙasarsu, don yă ba ku ita ta zama gādonku, kamar yadda yake a yau.
39 Sache donc aujourd'hui, et rappelle dans ton cœur, que l'Eternel est celui [qui est] Dieu dans les cieux, et sur la terre, [et] qu'il n'y en a point d'autre.
Ku sani, ku kuma riƙe a zuciya a wannan rana, cewa Ubangiji shi ne Allah a sama da kuma a ƙasa. Babu wani kuma.
40 Garde donc ses statuts et ses commandements que je te prescris aujourd'hui, afin que tu prospères, toi, et tes enfants après toi, et que tu prolonges tes jours sur la terre que le Seigneur ton Dieu te donne pour toujours.
Ku kiyaye ƙa’idodi da umarnai, waɗanda nake ba ku a yau, domin zaman lafiyarku da kuma na zuriyarku bayan ba ku, domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku har abada.
41 Alors Moïse sépara trois villes au deçà du Jourdain vers le soleil levant;
Sa’an nan Musa ya keɓe birane uku gabas da Urdun,
42 Afin que le meurtrier qui aurait tué son prochain par mégarde, et sans l'avoir haï auparavant, s'y retirât; et que fuyant en l'une de ces villes-là, il eût sa vie sauve.
waɗanda duk wanda ya yi kisankai, in ba da gangan ba ne ya kashe maƙwabcinsa, wanda babu ƙiyayya tsakaninsu a dā, zai iya gudu zuwa. Zai iya gudu zuwa cikin ɗaya daga waɗannan birane, yă tsira da ransa.
43 [Savoir], Betser au désert, en la contrée du plat pays, dans [la portion] des Rubénites; Ramoth en Galaad, dans [la portion] des Gadites; et Golan en Basan, dans [celle] de ceux de Manassé.
Biranen kuwa su ne, Bezer a dutsen hamada, don mutanen Ruben; Ramot Gileyad, don mutanen Gad; da kuma Golan a Bashan, don mutanen Manasse.
44 Or c'est ici la Loi que Moïse proposa aux enfants d'Israël;
Wannan ita ce dokar da Musa ya sa a gaban Isra’ilawa.
45 Les témoignages, les statuts, et les droits que Moïse exposa aux enfants d'Israël, après qu'ils furent sortis d'Egypte;
Waɗannan su ne farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Musa ya ba su, sa’ad da suka fito daga Masar.
46 Au deçà du Jourdain, en la vallée, qui est vis-à-vis de Beth-Péhor, au pays de Sihon, Roi des Amorrhéens, qui demeurait en Hesbon, lequel Moïse et les enfants d'Israël avaient battu après être sortis d'Egypte.
Sa’ad da suke a kwari kusa da Bet-Feyor, gabas da Urdun, a ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, da Musa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi sa’ad da suka fito daga Masar.
47 Et ils possédèrent son pays avec le pays de Hog, Roi de Basan, deux Rois des Amorrhéens qui étaient au deçà du Jourdain, [vers] le soleil levant.
Suka mallaki ƙasarsa da kuma ƙasar Og sarkin Bashan, sarakuna biyu na Amoriyawa, gabas da Urdun.
48 Depuis Haroher, qui est sur le bord du torrent d'Arnon, jusqu'à la montagne de Sion, qui est Hermon.
Wannan ƙasa ta tashi daga Arower a kewayen Kwarin Arnon zuwa Dutsen Siyon (wato, Hermon),
49 Et toute la campagne au deçà du Jourdain vers l'Orient, jusqu'à la mer de la campagne, sous Asdoth de Pisga.
ya kuma haɗa da dukan Araba gabas da Urdun, har zuwa tekun Araba a gindin gangaren Fisga.

< Deutéronome 4 >