< Deutéronome 20 >

1 Quand tu iras à la guerre contre tes ennemis, et que tu verras des chevaux et des chariots, et un peuple plus grand que toi, n'aie point peur d'eux, car l'Eternel ton Dieu qui t'a fait monter hors du pays d'Egypte, [est] avec toi.
Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, kuka ga dawakai da kekunan yaƙi da kuma mayaƙan da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu, domin Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar zai kasance tare da ku.
2 Et quand il faudra s'approcher pour combattre, le Sacrificateur s'avancera, et parlera au peuple,
Sa’ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist yă zo gaba yă yi wa mayaƙan jawabi.
3 Et leur dira: Ecoute Israël: Vous vous approchez aujourd'hui pour combattre vos ennemis; que votre cœur ne soit point lâche, ne craignez point, ne soyez point épouvantés, ne soyez point effrayés à cause d'eux.
Zai ce, “Ku ji, ya Isra’ila, yau kuna gab da kama da abokan gābanku. Kada ku karai, ko ku ji tsoro; kada ku firgita, ko ku yi rawar jiki a gabansu.
4 Car l'Eternel votre Dieu marche avec vous, pour combattre pour vous contre vos ennemis, [et] pour vous conserver.
Gama Ubangiji Allahnku, yana tafe tare da ku, zai yaƙi abokan gābanku dominku, yă ba ku nasara.”
5 Alors les Officiers parleront au peuple, en disant: Qui est celui qui a bâti une maison neuve, et ne l'a point dédiée? qu'il s'en aille, et s'en retourne en sa maison, de peur qu'il ne meure en la bataille, et qu'un autre ne la dédie.
Hafsoshi za su ce wa mayaƙa, “Ko akwai wanda ya gina sabon gida bai kuma buɗe shi ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă buɗe shi.
6 Et qui est celui qui a planté une vigne, et n'en a point encore cueilli le fruit? qu'il s'en aille, et s'en retourne en sa maison, de peur qu'il ne meure en la bataille, et qu'un autre n'en cueille le fruit.
Ko akwai wani da ya shuka inabi, bai kuwa fara jin daɗinsa ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă ji daɗinsa.
7 Et qui est celui qui a fiancé une femme, et ne l'a point épousée? qu'il s'en aille, et s'en retourne en sa maison, de peur qu'il ne meure en la bataille, et qu'un autre ne l'épouse.
Ko akwai wani da aka yi masa alkawarin mata, bai kuwa aure ta ko ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă aure ta.”
8 Et les officiers continueront à parler au peuple, et diront: Si quelqu'un est timide et lâche, qu'il s'en aille, et s'en retourne en sa maison, de peur que le cœur de ses frères ne se fonde comme le sien.
Sa’an nan hafsoshin za su ƙara da cewa, “Ko akwai wani da yake tsoro, ko ya karai? Bari yă tafi gida don kada’yan’uwansa su karai su ma.”
9 Et aussitôt que les officiers auront achevé de parler au peuple, ils rangeront les chefs des bandes à la tête de chaque troupe.
Sa’ad da hafsoshin suka gama magana da mayaƙan, sai su naɗa komandodi a kansu.
10 Quand tu t'approcheras d'une ville pour lui faire la guerre, tu lui présenteras la paix.
Sa’ad da kuka haura don ku fāɗa wa birni, sai ku fara neman garin da salama.
11 Et si elle te fait une réponse de paix, et t'ouvre [les portes], tout le peuple qui sera trouvé dedans, te sera tributaire, et sujet.
In sun yarda da salamar, suka buɗe ƙofofin garinsu, to, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su kuma yi muku aiki.
12 Mais si elle ne traite pas avec toi, et qu'elle fasse la guerre contre toi, alors tu mettras le siège contr'elle.
In kuwa suka ƙi salamar, suka fāɗa muku da yaƙi, sai ku yi wa wannan birni ƙawanya.
13 Et quand l'Eternel ton Dieu l'aura livrée entre tes mains, tu feras passer au fil de l'épée tous les hommes qui s'y trouveront.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba da shi cikin hannunku, sai ku kashe dukan mazan da suke cikinsa da takobi.
14 [Réservant] seulement les femmes, et les petits enfants. Et quant aux bêtes, et tout ce qui sera dans la ville, [savoir] tout son butin, tu le pilleras pour toi; et tu mangeras le butin de tes ennemis, que l'Eternel ton Dieu t'aura donné.
Game da mata, yara, dabbobi da kuma sauran abubuwan da suke cikin birnin, za ku iya kwasa waɗannan a matsayin ganima wa kanku. Za ku kuma yi amfani da ganimar da Ubangiji Allahnku ya ba ku daga abokan gābanku.
15 Tu en feras ainsi à toutes les villes qui sont fort éloignées de toi; lesquelles ne [sont] point des villes de ces nations-ci;
Haka za ku yi da dukan biranen da suke nesa da ku, waɗanda kuma ba na al’ummai da suke kusa ba.
16 Mais tu ne laisseras vivre personne qui soit des villes de ces peuples que l'Eternel ton Dieu te donne en héritage.
Amma fa, a cikin biranen al’ummai da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kada ku bar wani abu mai numfashi da rai.
17 Car tu ne manqueras point de les détruire à la façon de l'interdit, [savoir] les Héthiens, les Amorrhéens, les Cananéens, les Phérésiens, les Héviens, les Jébusiens, comme l'Eternel ton Dieu te l'a commandé.
Ku hallaka su ƙaƙaf, wato, Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa, yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku.
18 Afin qu'ils ne vous apprennent point à faire selon toutes les abominations qu'ils ont faites à leurs dieux, et que vous ne péchiez point contre l'Eternel votre Dieu.
In ba haka ba, za su koya muku ku bi dukan abubuwan banƙyaman da suke yi, ta yin sujada wa allolinsu, ta haka kuwa ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi.
19 Quand tu tiendras une ville assiégée durant plusieurs jours, en la battant pour la prendre, tu ne détruiras point ses arbres à coups de cognée, parce que tu en pourras manger; c'est pourquoi tu ne les couperas point; car l'arbre des champs [est-il] un homme, pour entrer dans la forteresse.
Sa’ad da kuka yi wa birni ƙawanya kuka daɗe, kuka yi ta yaƙi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari, domin za ku ci’ya’yansu. Kada ku sassare su. Gama itatuwan da suke cikin gonaki, ba mutane ne da za ku yi musu ƙawanya?
20 Mais seulement tu détruiras et tu couperas les arbres que tu connaîtras n'être point des arbres fruitiers; et tu en bâtiras des forts contre la ville qui te fait la guerre, jusqu'à ce qu'elle soit subjuguée.
Amma fa, za ku iya sassare itatuwan da kuka sani ba sa ba da’ya’ya, ku kuma yi amfani da su don ayyukan gina ƙawanyar, sai an ci birnin da yaƙi.

< Deutéronome 20 >